AUREN WATA SHIDA

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ



Story & written
       By mmn
        Fareesa


GODIYA... godiya ta tabbata  ga ALLAH (S W T) tsira da amincin ALLAH su tabbata ga annabi (S A W) da ahlayensa d sahabbansa .


GARGADI...banyarda wani ko wata yajuyamun novel ta kowacce sigaba.in kunne yaji ,jiki ya tsira..


BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM


P1

Not edited

Kyawawan Yan mata ne guda3  ketafiya anutse.suna fira ko waccensu hannunta rik'e da tulu da alama d'ibar ruwa zasu..
   Mitsss wadda ake Kira mero acikinsu taja tsaki "sakamakon hango dabar samarin karkarar tasu datayi"hade da cewa Ni wlh banison bi tanan haryar,sbd yarima HAMZA da abokansa kunsan ba mutumin kirkibane bbu abinda ya aje sai yima Yan mata da zawara FYAD'E Kuma mai gari yasani amma ya k'yalesa...yo har matan auren bebariba wlh cewar indo"yyinda RIYANATU dake gefe batace komaiba."
K'arasowarsu gab dasu yarima HAMZA yasasu yin shiru hade da yin sauri Dan suwuce lfy"Dan beda mutunci.
Yarima kuwa Yana atsakkiyarsu Yana isa da gadarar shi. Wai shi Dan boko Kuma D'an me gari,sbd duk k'auyen acikin samari bbu Wanda yakaisa ilimin boko da wayewa dg shi sai GALI..tun dg nesa idonsa yasauka kan riyanatu dake tafiya cikin nutsuwa da sanyin hali hade da kamun Kai"
..bbu bata lokaci yasaka yaronsa guda yatsaidata..
    Yan mata yarima HAMZA na mgn ! yafad'a yana nuna riyanatu dake tafiya bata ko kallesaba,yyinda su indo jikinsu ke kakkarwa sbd tsoro suna kallon riyanatu datak'i tsayaawa...yaron yyi saurin tare gabanta...wata doguwar tsuka taja hade da aikomasa da harara ta wuce abinta... kallon mamaki su indo suka bita dashi , yyinda yaron yanufi gun yarima HAMZA Dan sanar masa.


     Tun kafin yyi mgn yarima yad'aga Masa hannu alamar beson ji sbd duk abinda riyanatu tayi akan idonsa..
    Lumshe ido yyi Yana mugun mamakin wannan yarinyar Yar uban waye ce agarin nan be?" kamarshi yasa atsaida ita tak'i tsayawa sbd ita t isa...mittsss yaja tsaki hade da mik'ewa tsaye da nufin tafiya, yyinda yaransa suka tashi ,ya girgiza Masu kai . alamar beson abisa...salisu abokinsa dake gefe  yace Kai gsky yarinyar can Yar renin wayoce wlh lallai mutumin batasanka bane shiyasa...wani munafikin murmushi yarima yyi hade da cewa hmmm yau kau zata sanni Dan wlh yau din nan sai na rabata da darajarta Dan agarin nan bbu macen data isa tamun haka ...bejira amsarsaba da sauran abokansa daketa mgn yabi bayansu riyanatu..


Bangarensu riyanatu kuwa suna barin  Gurin su indo suka kama mata fad'a kan miyasa tayi hakan?"bacin tasan ko waye yarima da mugun halinsa Amma hartayi wannan abin.,,,,

Cikin dakiya tace be isa yamun abinda ALLAH bemunba bana tsoronsa ko kad'an Dan haka kubar maganar.

"Mairo tace inda zakiji riyanatu kije kibasa hakuri sbd gudun abinda zaije yafaru Dan ALLAH"

Murmushi riyanatu tayi mai sauti tace hmmm mairo kenan bbu inda zani balle har nabasa hakuri Dan banmasa laifi ba"indo tace Amma dakin sani baki k'i tsyawa...aitariga ta makara tunda har ta rigada tayi mun haka nikuawa ayau Zaki gane bakida wayo ko ke Yar uban waye agarin nan...cewar yarima a hassale cikin fushi"

Gaba d'aya suka juya banda riyanatu suna kallon sa...cikin bacin rai riyanatu tace dakata mlm kada kasake hadawa da iyayena ,ubanah na kabarinsa dan ha.....saukar Marin dataji yasakata yin shiru tana kallonsa" nunata yyi da yatsa  hade da cewa lallai yarinya bakinki yajamiki ke har kin isa Ina mgn ki mayarmun to wlh yau saikinyi nadamar haihuwarki a k'auyen nan fuuuuu ya wuce abinsa... yyinda riyanatu dake rik'e da kunci tana kuka hawaye ya wanke mata fuska,nan su indo suka ba ta hkr hade da cewa data sani ta tsaya Allah yasa kada yyimata mugun Abu Dan sun tsorata da kalaminshi ,Amma ita bbu hakan atare da ita.

Byn sun gama d'ibar ruwan ko wacce ta wuce gidansu jiki asanyaye.

Riyanatu kuwa ko afuska bata nuna ma umma komaiba,Amma Abu daya yatsaya mata arai ,shine sai kinyi danasanin haihuwarki agarinan yau...,byn ta aje ruwan," nan tashiga hidimar aza girkin dare Wanda da k'yar umman tahada kudin akasiyo abin bukata sudafa sbd basu dashi.
     Sai gab da magrib ta ida tuwan ta gyara Gurin tayi alwarlal magrib ta nufi daki ta data Sallah"
Itama umma alwarlal ta Fara tana Duke taji anyi sallama"ta d'ago tana amsa fuska asake sbd ganin gali D'an aminiyarta ,saidai jikinta yyi sanyi ganin arikice yashigo gidan
Ko gaisawa basuyiba arude yace umma Ina riyanatu?"

"Da sauri tace lfy dai ki?"

Arikice yace bbu umma ,Dan ALLAH duk yadda  zaayi cikin 2 kuyi guda ko kubar garin nan ko kada ku kwana agidan nan...

Cikin kosawa umma tace dan ALLAH kamun bayani mana! Sbd mezamubar  gd?"

"Gali yace sbd yarima HAMZA nason yaketawa riyanatu haddin ta"

Inna lilahi wa Inna ilaihir Raju un" umma ta fad'a tana kuka,hade da cewa akan wane dalili,ko kuwa  hakanan sbd zalinci anganta arainiya ko??"

Cikin tausayinsu gali yashiga  sanar da ita komai kasan cewar agabansa yarima HAMZA yyi maganar,Amma be nuna  yasan riyanatu ba kuma( Yana sonta be nuna mata)hakan yasa hankalinsa tashi sbd yasan yarima mugun busurune...

Sannan yyi ajiyar zuciya yace umma ga shawara ..adedenan riyanatu ta fito dg daki da alamar ta idar da sallar ta nufosu tana kuka..

Da sauri umma taceinajinka"

Yace muje gidanmu ku kwana scan kafin da asuba kubar garin sbd wlh kinsan zai iyayin komai akanku sbd ubansa bazaice Masa komaiba "

Umma da riyanatu na kuka suka kwashe kayan sawarsu agana,da abinda suke bukata suka saka a buhu ,Saida akashiga sallar isha'i sannan suka kwashe kayan su ,sukabar ledar k'asa d katifa suka rufe gida hade da nufar gidan Inna mariya mahaifiyar gali,yyinda uma gabanta ke faduwa svd batason wane gari zasu ?"kauye ko birni?"Dan xuwarta bunni guda alokacin yayarta nacan to yaxu Kuma batasan Ina yayarta takeba ta mutu ko tana raye..

 
Da wannan tunanin aran umma,suka iso gidan Inna mariya, yyinda riyanatu keta kuka da adduar ALLAH yakubutar da ita dg sharrin yarima.

Byn zuwansu gidan  gali ya ma inna bayani ,salati tayi sbd ta tsorata.  ta kalli umma  tace ki kwantar da hankalinki  bintu insha ALLAH zaku kub'uta sbd inaji ajiki na barinku garin nan alkhairi ne babba,Zan Kira wata zuwaira inada number ta agarin kaduna take can zakuje insha  ALLAH zata baku masauki ta nuna muku gari Dan gaskiya nabaki goyan bayan kubar garin nan sbd martabar y'ar ki guda aduniya tak...

Ajiyar zuciya umma tayi tace to nagode sosai ALLAH yabiya.

Inna tace amin byn komai yalafa zan je nasanar da baffan riyanatu, sannan akwai kudi gurunku?"

Umma tace eh a"akwai dubu ukku"

Inna tace zanbaki dubu5 ,kukara sbd ai Sanaa Zaki samu acan harki maida riyanatu makaranta ko?"

Umma tace eh nagode mariya,Amma akwai busashena zasuyi kudi mai kauri kisiyarmun gali yakaimun kudin "inna tace to,yyinda riyanatu keta kallon su tana tunanin zasubar garinsu zuwa wani gari sbd wani banxa Allah yasa hakan shiyafi alkhairi...


Nan Inna ta sa gali ya Kira mata ita da wayarsa.


Bbu bata lokaci Inna ta amsa tayiwa zuwaira mai abinci bayanin zuwansu riyanatu d mahaifiyar ta , tace ALLAH yaka wosu lfy.

Nan Inna ta  musu kwatance insun iso garin yadda zasu gane..


Shikuwa gali yaso yaja riyanatu yafad'a mata sirrin  zuciyarsa kafin su tafi amma ganin su Inna sai yafasa.


Washe gari tunda asalati su umma sukayi ban kwana da mariya,gali yadaukar musu wasu dg cikin kayansu,yyi musu rakkiya sbd duk ana masallaci bbu Wanda yagansu ,dukda atsorace suke.

Be barsuba Saida suka yi tfiya mai nisa har suka iso titi  suka hau acaba sannan yajuya yafafi  cike d kewar su hade d tausayinsu..alokacin har gari yafara haske...

Bangaren yarima HAMZA kuwa da misalin karfe 2:00 am yanufi gidansu riyanatu da yaronsa da yasaka yabinciko Masa gdn su.

Suna zuwa....๐Ÿ˜‡๐Ÿ˜‡

Yawan comments yawan typing.


Share pls


BY MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


  Story & written
By mmn fareesa

Not edited

Dedicate to my lovely sister hauwau u lado๐Ÿ˜‡๐Ÿ˜‡

P2

....Suna zuwa gidan suka haura ta katanga , yyinda yarima yasanar da yaronsa yatsaya tsakar gd shi yashiga dg ciki.
      D'akin dake bud'e ya kutsa Kai ciki Yana dariyar mugunta....turus yyi ganin dakin wayam bbu alamar da mutane aciki sbd yahaske ko Ina da fitila"da sauri yafito Yana cewa taf lallai meke Shirin faruwane?"
Yallab'ai lfy dai ko?"
Cikin takaici yace tabbas akwai Wanda yasanar da ita da iyayenta zuwa na "amma muddin Ina raye akuma garinnan take to dole burina yacika...
    Fuuuuu suka fice dg gidan rai bace.

Zuwa safiya gari yakarad'e riyanatu sun gudu da ummanta,wasu na tausayinsu wasu na tsinewa yarima sbd dalilinsa suka gudu...

Koda baffan riyanatu yaji wanna an lbari da kanin ummanta hankalinsu yatshi matuka sunyi nadamar zamansu garin da me garin garin baya adalciko kad'an, D'ansa na bata d'iyan jamaa amma baya mishi  mgn ko tsawatar Masa...


############

K'amshine daddad'a ke tashi a parlourn na turarukan wuta dna air freshener"kallo daya zakama parlourn kasan mamallakansa naira tana kuka agurinsu yahadu ya k'awatu.
Wasu masu aikine suka shigo da warmers ahannunsu suna jerawa akan dining table din dkae cikin parlourn...wata hamshakiyar mace ce ta fito cikin shiga ta alfarma tana yauki had'e da  takun izza,Yar kimanin shekara45 xuwa 47 ."
Cikin girmama had'e da rawar jiki sukace ranki yadad'e ankammala! Cikin bada order ta yatsina fuska  tace Ina fatan komai very need sbd kunsan my son akwai k'yankyami,Dan munyi waya yanxun yace sun kusa k'arasowa.
Wacce ake Kira da hassu tace insha ALLAH komai yyi lfy yadda kikeso hjy...kafin tayi mgn sunji karar motoci da alamar Wanda ake ma liyafar ya iso, da sauri ta sallamesu, sannan ta nufi kofar fita dg waiting parlou tana wani murmushi Wanda bansan ma'anarsaba..

Gaba d'aya body guard d'insane suka Fara fitowa,shikuwa  ogan nasu be fitoba.wata haddiyar motace dake tsakkiyar motocin ita aka bude gidan baya...wani fitinan  nan kamshi me saka nishadi yafara gauraye Gurin, kafin santala santalan kafafunsa su bayyana sanye da takalmi sawu ciki . ahankali ya ida fitowa...
Wow Masha ALLAH nafad'a azuciya ta sbd  ganin guy din hmmm ALLAH yyi baiwar halitta agun kyakykwa wane ajin farko dogo fari...suit ne bak'ak'e ajikinsa Wanda suka haska farar fatarsa da agogo baka daure atsintsiyar hannunsa ,yyinda kansa yasha gyara sai salk'i yake lolx..
     Fuska bbu walwala yarika amsa gaisuwar ma'aikatan gdn,daketa aikin gaidasa,sannan cikin takunsa na isa yake tafiya tamkar bayason taka qasa..tuni guard's d'insa suka Fara kokarin binsa .
da hannu yyi musu alamar ah ah hakan yasasu dakatawa dg binsa..
Adede step din da zai sadasa da waiting parlou yahadu da momynsa... murmushi yyi hade da nufarta Yana cewa i miss you my lovely mom..
Dariya tayi ta rungumesa suka shige cikin parlourn.;;;


Kan 2 seater yazauna Yana k'arewa parlourn kallon yaushe gamo"kafin su gaisa da mom Yana tambayarta  abbansa.

"Tace Yana hanyar isowa gdn"

Tamkar wani yaro ya shagwabe fuska had'e da cewa gsky Abba yadena ji Dani gsky mom ,sbd ai dayazo tarata ko yajira zuwana agd in bezo air port ba"
Murmushi tayi hade da cewa hmmm my son yanxunfa ka girma sai Shirin aje iyali kake amma kak'i barin shagwaba ko ?" To ai munatare dashi jiranka ,akamasa Kiran gaggawa a office shiyasa.
       Had'e rai yyi hade da cewa Ni gsky mom Adena maganar na wani aje iyali dududu shekarata nawa daza'amun aure ne?" bacin kinsan ma zeenat din da kikeso ki auramun sai nan da sheraka 2 zata gama skul Kuma ake tada mgnar yanxun .
Girgiza Masa Kai tayi tace hakane ALLAH yakaimu lokacin ,yanxun tashi muje kayi lunch ko.

Agogon hannunsa ya duba yace NO mom bara nayi wanka tukum"Ina fatan komai yyi mun ?"kinsan bansan kazanta.

"Ahankali ta ce oh me hali baya barin halinsa"ABDALLAH komai yyi need kaje kaduba , shiyasa ma nasaka harira ta nemomun mai aikin dazata ruk'a kulamun dakai kafin kayi aure tunda ni Ina office...kafin yyi mgn abbansa yyi sallama.

Da sauri yatashi Yana murmushi ya rungumesa, yyinda abban ke dariya Yana d'anbuga bayansa Yana cewa my son Kai baka girma ko?"

Shima dariyar yyi yace eh Mana tunda banida kani ko yayaba, yafad'a yana sakin abban ,yyinda mom tayi tamkar bata parlourn.

Abban ne yakalleta Kai Duke yace hjy nadawo ,cikin ko inkula tace ok Ni zanshiga ciki kafin yarona yayi wanka ,akwai inners dina dake a toilet ka wankesu su fita kasan na jiyama basu fitaba ....fuska asake Abba yace to ,bacin wanki bbu aikin dazanmiki?"
Iya nan ABDALLAH yaji yabar parlourn Yana huci.
Tunanani yake azuciyarsa ,dama har yanxun momynsa Bata Dena juya abbansaba ke nan?" Sbd tsawon shekara4 kenan baya k'asar Yana ingila,Ashe bata bariba...wani mugun tsaki yaja afili yace bazan iyaba saina Miki mgn harda abban shima.

Wai meke faruwa ne,miyasa take Masa haka??"shikuma Yana binta tamkar shine matar itace mijin ,cikin bacin rai ya isa part nasa.

Duk yadda ma aikatan suka yi kok'arin gyara part d'in Amma shi be masaba sai ma yaja tsaki rai bbu Dadi yyi wankan yasaka jallafiyya Fara had'e da feshe jikinsa turarukan sa .yanufi masjeed sbd time din sallar azuhur yyi...


   ********************
Su riyanatu kuwa byn sun sauka dg acab'an dayakaisu Tasha ,bbu bata lokaci suka hau motar kaduna.saida sukayi tafiyar awa6 amota tukum sannan suka iso kasancewar dg garinsu zuwa nan da nisa sosai.

Tun a Tasha suke raba ido abunka da Wanda ke bako, riyanatu ta tambayi wasu dattijai inane unguwar kawo?" Su bak'i ne....

Nan akasamu mai adaidai aka fad'a Masa inda zai kaisu .

Har kofar gidan zuwaira me abinci aka aje su,sbd tayi suna agarin duk asanta shiyasa basu wahalaba.

Amatukar gajiye da yunwa suka yi sallama asoron gidan da jamaa keta cin abincin Rana da alokacin befi karfe3 ba na Rana.

Sai kallon su ake ganinsu da gana d buhu ansan matafiya nesu , sannan Kuma kauyawa dukda ba irin kauyawannan neba sosai sbd riyanatu tayi boko akauyen su.

Cikin sakin fuska suka ida  shiga ciki da sallama .
Ko da zuwaira tagansu tuni taganesu ta amsa da faraa tana musu maraba.

Nan taimusu iso ciki suka ci abinci sukasha ruwa , sannan suka yi Sallah.

Zuwaira tabasu wani daki karami agdn tace su saka kayansu suyi wanka su huta ,inta gama sallamar customers sunyi mgn .

Amsawa sukayi suna mata godiya da wannan karamcin data musu..,,,,

Ana idar da sallar yanufi gd.

Part d'in mom yanufa fuska bbu walwala yyi sallama can ciki ciki.

Mom ta amsa.....


Share pls


BY MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story & written by 
Mmn fareesa

P3


"""Mom ta amsa tana kallonsa had'e da mik'ewa tsaye tana cewa kada womy son?"
Muje ko kaci abinci,fuska bbu yabo bbu fallasa ya amsa da to mom muje.. dining area suka nufa a tare.
Zama sukayi kafin  tafara serving nasa.
      Haka yake cin abincin suna fira da mom jefi jefi yake mgn dan shi mutum ne dabaya son yawan surutu da mgn,saidai fa ta lura D'an nata na cikin damuwa Amma taki tambayarsa damuwarsa .
da haka ya ida cin abincin ya Mike had'e da cewa mom bara naje part dina munyi da Hafiz zaizo yanxun...katse sa tayi dacewa atsawace  hmmm kana nufin Hafiz yafini k'ima a gurinka ,Ina matsayin mahaifiyar ka har wani banxa yafini  daraja agunka ,shekara4 bamu haduba Amma baza ka zauna mu gaisa muyi firar yaushe gamo...iye?"nifa banason abotarku da shegen yaron nan Yana fama da tsawo uwa daran Sallah mitss taja tsaki hade da yin kwafa..
Mamaki abdallah keyi azuciyarsa ,shidai yasan Hafiz bashida  wani aibu ko wani mugu hali ,hasalima tun tuni Hafiz naba shi shawarar kwarai da fad'a Masa gsky Amma yalura mom batason abotarsu... K'arara take nunawa Hafiz k'ii.. Wai badakai nakeba ?" Kamun shiru!
     Kafin yyi mgn abbansa yashigo parlourn da sallama, Abdallah y amsa Yana murmushi had'e d hugging abbansa Yana cewa Abba bara naje part d'ina nadawo mu sake gaisawa.
Sannan ya juyo Yana kallon mom ke musu wani kallo mai wuyar fassara yace pls mom i am really very sorry! bejira amsartaba yafice Yana tambayar kansa miyasa yafison abbansa da tausayinsa akan mom bacin ance duk d'a yafison uwarsa akan ubansa..

Da wannan tunanin ya isa part nasa"

Murmushi yyi sakamakon hango Hafiz dake zaune kan 2 seater .

Shima Hafiz tashi yyi Yana dariya had'e da hugging abokin nasa dayake masifar kauna yyi, sannan suka yi musabiha suka zauna had'e da Fara firan yaushe gomo.

Abdallah yakalli agogon dakin yace friend time din sallar la'asar yakusafa!

Y'ar dariya Hafiz yyi hade da cewa hmmm big man kenan Ashe har yanxun halayenka masu kyau nanan?" zuwanka turai bai canzakaba ko?"

Harararsa Abdallah yyi yace Kai Dan iskane wlh to Dan mutum yafita waje sai yacan za halaye .

Amma ai kasan akwai masu canzawa,bama wannan ba kasan bikinmu my feedo ,saura 3 weeks Kuma sbd Kai nakara Masa tsawo Dan biki bbu aminin ango ai bazaiyi armashiba, kaga kaima dg nan ai sakasamu wata fine baby ko jone ko?"cewar Hafiz Yana dariyar shakiyanci...
Tsaki abdallah yaja had'e da cewa hmmm kaifa matsalata dakai kenan wlh bakada mgn sai ta mata ai gara su ammi suyi maka aure wlh sbd jarabarka kada wata Rana ka Fara  kama ya'yan mutane wlh ,sbd nason inkana mafarki da sabbatun....look mlm dallahai gara Ni dakai,tunda Kai boye taka jarabar kake amma saika rik'a basarwa,garama ka falka dg bacci cikin  y'an matan dake tururuwar cewa suna  sonka ka fitar da guda musha biki kawai..
Harararsa yyi cikin kosawa yace hmm aini har yanxun Banga macen data isa nace inasontaba  bangantaba Dan duk basuyiminba ,ita xeenat tursasawar mom ce kawai yasani kulata da kokarin cusata araina Amma taki ta cusun.
         

      Shiru Hafiz yyyi danko shi kanshi wani time din Yana tunanin anya mom ce mahaifiyar Abdallah kuwa?"

Sallamar zeenat ce ta katse musu firarsu...tuni gogan naku yyi kicin kicin da fuska sbd ganin yadda tabayyana surar jikinta a fili Kuma Wai itace matar dazai aura..

"Sanye take da riga da wando sun matseta kirjinta have waje "ga gashin doki da tayi attached  dashi ,tasaka wani siririn mayafi dashi gara bbu,sai fitinan nan kamshi ketashi ajikinta.

Hafiz ne yyi kokarin danne dariyarsa sbd ganin yanda Abdallah yahade rai,ya amsa sallamar ta, had'e da cewa ranki yadad'e munyi fushi gsky sai yanxun zakizo ganinmu .

Murmushi tayi hade da cewa hmmm wlh ba laifina bane ,Saida na tambayi baby yaushene time din dazai sauka dg jirgi naje airport tararsa ,amma yaki fad'a.
ta fad'ar hakan had'e da nufar tana kokarin hugging nasa...wata zabura yyi hade da kaucewa tafad'a kan kujerar ,fuska bbu walwala tace meye haka baby?"
     Tabe bakiyyi beyi mgn yadubi hafis yabanko Masa harara sbd ganin Yana tarin k'arya akan dariya nason kuccemasa.
Cikin basarwa had'e da danne zuciyarsa yace my zeenat ya kk ya su ummi ??"  
   Lumshe ido tayi sbd jin sansanyar muryarsa mesata nishadi,tuni ta nemi bacin ranta ta rasa"ahankali ta ce lfy lau alhmdllh gsky baby kayi kyau Zama ingila ya karbe ka dukda wani time din Muna video call ,amma sainaga kafi kyau azahiri.
Murmushn gefen Baki yyi hade da mik'ewa tsaye sbd tuni Hafiz yabasu guri gudun kada yyi katib'ara..
Ya dubeta ,cikin k'osawa da surutunta yace my zeenat zamu wuce masjid dg nan ...amma aizaku dawo Zan jiraka pls shekara4 fa bamu haduba,tayi saurin katse Masa mgn,adakile yace dg masjid akwai inda zani..amma baby b....pls ya isah banason surutu kada kisamun ciwon Kai malama .hmmmm kodai gun wata zakaje ,inkuwa hakn yafaru wlh zatayi nadama yarinyar sbd indai akankane to wlh har kasheta Zan iya yi sbd....stop it Abdallah yakatseta atsawace, had'e da ficewa dg parlourn fuska daure.
Tsaki yaja azuciyarsa yace shiyasa banson xaman Nigeria gashi tun ban kwana ba Raina na baci,wlh taci darajar mom shiyasa nike binta ahankali sbd gudun b'acin ran mahaifiyata da wlh sai tagane kuranta ,sbd rashin hankali Wai zata iya kisa mittss yasake Jan doguwar tsuka....Hafiz dake kallon sa yace lfy dai ko AK(haka abokansa ke kiransa) naga kana tsaki ko kaida madam ne?"
wata uwar harara ya maka Masa suka fice zuwa masjid, yyinda Hafiz yyi shiru sbd yasan halin abokinsa.;;;;



Da dare byn yagama isha'i sannan yanufi part din abbansa.

Byn sun gama gaisawa atare sukayi diner da Abba sannan suka Fara fira .

Can Abdallah yace Abba Wai Dan ALLAH miyasa baka zuwa bauci Kuma bakason naje??" bacin kasan danginkane acan pls ka amsamun .

Shiru Abba yyi hade da Jan numfashi , sannan yashe kayi hkri nima bansan daliliba ,amma very soon zamuje tare amma kada kasake kayiwa mominka wannan zancan kaji?"

Cikin mamaki abdallah yace miyasa Abba?" 

Kallon sa Abba yyi yace kayi hakuri banason tambayar kaji ?"shiru Abdallah yyi Yana tunanin Wai Mike faruwa ne tsakanin Abba da danginsa daya mantadasu baya taimakonsu da d'inbin dukiyarsa".

Kallon Abba yyi cikin marairai cewa yace pls my Abba Zan maka wata tambaya "

Kallon sa Abba yyi hade da tsaresa da ido yace inajinka"

Fuska bbu walwala yace Abba miyasa kake bin umarnin momy saikace Kaine mijin itace matar?"gsky Abba abun namun ciwo inda Momi ba mahaifiyata bace dole karabu da ita,sbd bazanso ganin ana juyaka ba Abba why?"yafad'a cikin 'bacin rai ,idanunsa sunyi jajir, yyinda Abba yakasa mgn dabashi amsar tambayar sa.

Cikin huci yace shiyasa banson aure sbd abinda mom ke maka Abba gsky ,dan bazan iya k'yale mace ta juyaniba,Kuma Ni xanmata mgn Abba sai....da sauri Abba yace kul!

Kada kasoma kaji abdallan Abba kamana addua komai zai daidaita zata denakaji insha ALLAH yafad'a cikin damuwa.

Kallon Abba yyi hade da cewa shikenan Abba baza n mata mgn ba.... murmushi Abba yyi yace ko kaifa my son .

Mamaki abdallah keyi azuciyarsa ganin Abba yasaki ransa jin Wai bazaiyiwa mom mgn ba lallai akwai abinda ke faruwa wanda besaniba ....

Besake ma Abba wata tambayar ba baci wannan haka sukayita firarsu har mom takira Abba a waya tukum sukayi sallama.

Part d'in sa yawuce, direct toilet yashige ,yafi 30 minit sannan yafito yyi Shirin kwanciya yafeshe jikinsa da turarukan sa masu masifar kamshi.

Tamkar zeenat najira ta yi kiransa,tsaki yaja ganin itace,saima yarufe wayar baki daya ,dama be dadeda saka sim card d'in sa ba na Nigeria.,,,,,


Bangaren su riyanatu kuwa"da dare byn sunyi komai harda Shirin kwanciya zuwaira ta shigo"
Bayan  ta sallami customers,da sallama ,ta zauna suka sake gaisawa sannan ta musu murnar kubutarsu dg garinsu..

Sannan tace to da farko dai mariya Yar uwatace, sannan nima mijina y mutu inada y'a zatayisaar wannan,ta nuna riyanatu dake zaune kan ta duke.

Tana makaranta kwana ajinta5 befi saura kwana 8tadawo hutuba nan dakintane kuke.

To yanxun wace Sanaa Zaki iya?"

Umma taja ajiyar tace ko aikatau nasamu lfy lau.

Zuwaira tace to shikenan ma sai kimun sbd memun wanke wanke tayi aure sati2 dasuka wuce,awata Ina Bata dubu ukku ,Kuma nikecida ta,Zaki iya?"

"Umma tace eh insha ALLAH"

Zuwaira tace to ita riyanatu tayi makaranta?"

Umma tace eh wlh dg aji 3 tabari,anata mun surutu Wai nabarta tana karatu bbu aure saita lalace ta girma ta gand'ame.

Murmushi zuwaira tayi tace hmmm in bacin abin mutumin kauye duka riyanatu nawa take,ai batawuce 17 ko 18 ko?" 

Umma tace eh"

Zuwaira tace to shikenan insha ALLAH in sun koma huta sai a maida ita da islamiya ko?

Umma tace eh ,acan ta allo takezuwa tayi ihu34 .

Zuwaira tace Masha ALLAH.

Nan sukayi sallama ta basu guri su sake.


Washe gari...

 Share pls


BY MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written
By mmn fareesa


Wannan shafin nakune halak malak
Bilkisu Auwal
Fatimatou
Queen
Kuyi yadda kukeso dashi comments naku yafi nakowa yimun ๐Ÿ˜„๐Ÿ˜❤

K'oRAFI...wasu dg cikin ku suna mun korafin Wai banfadi waye Abdallah ba da Kuma wacece riyanatu ba,musammun mmn shukra novel kunfi K'oRAFI. To kusani gsky banison gajan hakuri kubi komai ahankali zakuji ,dukafa pages3 akayi Amma anfaramun K'oRAFI,duk wadda taji bazata iyaba so pls tadena bina...

P4


'''"""washe gari misalin karfe 8:30 am Abdallah yafito cikin bacin rai da damuwa a fuskarsa"straight parlourn mom yanufa yasameta ita da masu aiki a dining area suna shirya breakfast .
     Koda ta lura da yanayinsa,tuni ta sallami masu aikin .byn sunfita yazo yazauna kusa da ita had'e da aza kansa agefen kafad'arta,cikin shagwaba yace good morning my mom! Murmushi tayi had'e da shafa kansa tace morning my son,yahbak'unta?" Turo baki yyi tamkar yaro yace gsky mom bazan iya Zama cikin dattiba,kwata kwata masu Miki aiki basu iyaba nifa nafison ko Ina nagansa need.... girgiza Kai tayi had'e da cewa pls my son kayi hakuri Zan sake Kiran harira ta sake bincikamun wacce zata ruk'a kularmun dakai,amma yanxun muje nahada maka ruwan wanka ,kafin ka fito nagyara inda kakeso kaji abdallan momy ta fad'a cikin rarrashi...
Murmushi yyi yace yauwa kokefa mom ,to Amma gaskiya me tsabta zaa samu ko Kuma marar surutu . sannan gsky momy intazo kiyi warning nata akaina danbanson shishgi.... fuska bbu walwala tace Wai yaushe zaka Dena wannan miskilancin nakane?"damafa jiya da zeenat tazo gunka haka tadawomun da kuka Wai ka shareta  kunyi tafiyarku kaida wannan yaron mittsss taja tsaki hade da cewa ni wlh narasa wacce jaraba ce wannan kudai ba gari daya kukeba aiki yakawosa anan iyayensa na kano,dg kunyi skul tare yazo yawani manne maka ,kilama shike turaka ka wulakanta zeenat...
Kallon mom yyi"ahankali yace kiyi hkri mom Hafiz bashida wani aibu ko wani mugun hali sai kyawawan halaye, sannan zeenat banmata komaiba, lokacin sallah yyi dalilin dayasa muka fice kenan,dg karshe mom zeenat batada tarbiyya da kamun Kai na ya'yan kwarai...
Ya isa haka kayi hakuri zata canza kasan dai uwarta kawatace ko?"to banison jin komai muje kayi wankan.
     Bbu musu yabita har part nasa.
Mom batabar part d'in ba. saida komai yyi yadda Abdallah keso tukum ta fito da niyar aiko Masa breakfast dinsa.,,,,,



      Bangarensu riyanatu kuwa ,cikin yadda ALLAH suka tashi da safe suka kimtsa hade da Karin kumallo , sannan umma ta Fara aikinta yyinda riyanatu ketayata.
    Azaman dasukayi da zuwaira dg jiya zuwa yau sun gane mace ce ita mai kirki dason jamaa,sbd duk wani Abu dazasuyi kauyanci akai ,zatayi saurin gyara musu shi cikin aminci  bbu tsangwama.


************
Abbane ketsaye gaban dressing mirro Yana fesa turaruka,yanata sauri da alama fitama zaiyi... Abdallah yyi sallama yashigo Yana murmushi had'e da kallon Abban nasa Yana gaisheshi,hade da cewa Abba office zakajene kk sauri?"
Juyowa yyi Yana dariya yace ah ah my son!wlh tafiyace ta kamamu harta tsawon 2 weeks Kuma tare da president zamuyita zuwa indiya dg nan mudawo Abuja muyi wani meeting tukum nadawo ,nima da safen nan byn nadawo dg masjid sakon tafiyar ya isomun jirgin karfe,9:am zamu hau...
      Fuska bbu walwala yace Abba gsky nidai banison katafi dudu yaub kwana na nawa a Nigeria?"murmushi Abba yyi hade da cewa sorry kaji my son nima naso mu zauna sbd inason to bude sabon kamfaninka kafara aiki ,karika fita office Amma insha ALLAH innadawo munyi mgnar..
Yafad'a had'e da daukar wata jaka, yyinda Abdallah yakarba da nufin Masa rakkiya.
A parking lot ne yakedubarsa ganin bbu momi amasu rakkiyar ,yace Wai Ina mom bazata maka rakkiyaba??"
Murmushi Abba yyi hade da cewa ah ah munyi bankwana ai da ita"Abdallah bece komaiba yyishiru har guards d'in Abba suka bude Masa gdn baya yashiga ,nan yarika dagawa Abba hannu had'e da Masa adduar sauka lfy..

        #####

Haka rayuwarsu umma da riyanatu ta kas canance agdn zuwaira mai abinci bbu kyara balle tsangwama har tsawon kwanaki 8
Ayaune Kuma suke jiranxuwan Fatima y'ar zuwaira dg skul kasancewar yau ake hutu ....

Zazzaune suke atsakar gd bacin sun gama aikin safe ,zuwaira nata yanka salad na abinci .wata dattijuwar mace tayi sallama , zuwaira ta amsa fuska sake tana cewa ah ah lallai harira b'atan Kai kikayi agidan nan?"
Murmushi harira ta yi tace hmmm ah ah wlh naxo mu gaisa ne andad'e baahad'uba ...

Nan suka gaisa da zuwaira, sannan umma tace Ina kwana?"

Harira ta amsa , had'e da cewa Masha ALLAH zuwaira Baki kikayine  agdn?"

Zuwaira tace eh Yar uwatace wannan yartace,banan suke ba ,Amma sundawo da zama agarin nan.,,

Harira ta ce Masha ALLAH"

Byn taci abinci sukayi sallama ta fice..

Harira batafi minti12 da fitaba saiga Fatima da masu daukar Mata kaya sunyi sallama.

Da gudu tajeta rungume  mamanta ,tana ihun murna, dariya zuwaira tayi tace to auta sakeni karki kadani ga Baki nan munyi Kuma goggonki ki gaishe d ita...

Juyowa tayi lahh Ina kwana ?" Waccan kyakykyawarfa mama?"ta fad'a tana nuna riyanatu dake kallon ta.

Murmushi zuwaira tayi tace y'ar uwarkice Kuma kawarki....ihun murna tayi had'e da zurawa aguje t rungume riyanatu sbd Fatima akwai son jamaa.

Ita riyanatu cikin murna ta tarbeta,kafin kace me,harsun shaku da juna,komai tare suke har aka kwana aka wuni ,tuni Fatima ta Fara kokarin wayar da riyanatu da koya Mata kwalliya duk da bbu abin kwalliyar Dan kayanta basufi kala7 ba ,suma kuma duk sunji jiki,hakan yasa Fatima tabata nata kala4 Kuma sabbi , sannan da kayan kwalliyar ta suke amfani...
Hmmmm acikin kwanakin duk Wanda yasan riyanatu a kauye to yaganta yanxun bazai ganetaba,sbd yadda ta canxa.
Dama gata da muguwar tsabta ,saidai matsalarta guda batason saka gyale saidai hijab.

Lokacin da Fatima ta koma islamiyya duk tadamu sbd ita agd ake barinta Kuma zaman gundurarta yake,Koda umma ta lura rarrashinta tayi had'e da cewa in wata yyi zata sakata Amma bacin wannan aikatau dole su nemi wani abun suyi.sbd sai wata yyi abasu kuma kafin zaka zasu iya bukatar wani Abu gakuma skul da akeson mayarda riyanatu,danma zuwaira na kokari akansu to Amma yau d gobe sai Allah.

**************
Mom ce zaune kan kujera ta aza k'afa daya kan daya ,ga lemun kwali gabanta kan center table tana kurba ,tana yatsina, yyinda tayi wani murmushi had'e da kallon matar dake zaune gefen kafafunta kan carpet tace to harira kinji dai dalilin. Kiranki Dan ALLAH kisamo mai tsabta, wacce zata kularmun da yaro Amma ba mai surutuba Kuma banison babba ,nabaki nan da kwana 2 Dan ALLAH kikamun ita muyi mgn nasanar da ita aikinta ,Amma banison mai yawan mgn da surutu gsky sbd my son bayason yawan mgn , sannan Kuma kikawo marar wayo sbd kinsan banison sa ido gsky...inhar kikayi yadda nikeso kinada kaso mai tsoka kema.


Ajiyar zuciya harira ta yi hade da cewa to ranki yadad'e insha ALLAH zaasamu Dede yadda kikeso.zan bincika dg yau zuwa gobe insha ALLAH.

Kafin mom tayi mgn Abdallah yashigo parlourn da sallama, sanye yake da suit farare ,yyi masifar kyau ,yyinda sallayar dake tsakkiyar goshinsa takara fitowa da Masa kyau ga sajensa yasha gyara sai kamshi take tashi ajikinsa tunkan ya ida isowa kamshinsa ya bayyana. kamar kulum fuska atamke yazauna Yana gaida mom had'e da cewa harira Ina yini?"

Baki washe ta amsa tana Masa kirari,yatsina fuska yyi yamike tsaye da nufin barin parlourn, adedenan zeenat tayi sallama sukayi 4 eyes da Abdallah tabe baki yyi hade da kauda Kai yyi haryar dazata sadasa da part nasa....

Mom ta yi saurin dakatardashi gurincewa haba my son !bak'uwa fa kayi zaka tafi kuma"

Cikin agree voice yace banason mgn da kowa sbd kaina na ciwo pls mom nafison kebantuwa,bejira asartaba yafice.

Yyinda mom ta sallami harira ta fice.

Byn fitar harira mom
Ta dubi zeenat dake kukace tace oh ni hafsatu mezan gani haka,sbd d'a namiji kke kuka da hawaye??" 


 gsky zeenat kin rako Mata aduniya,shiyasa yakemiki wulakancin daya gadama ,tunda yalura da yadda kikesonsa .

To bari kiji shi namiji baa Masa haka ,saikace ke ba rainon hjy kilima bace?"

To bari kiji dg yau kirike ajinki ,kina Abu kamar Baki lek'a ajiba ,ainariga nagayamasa kece zabinsa ,Dan haka ko zai mutu sai ya aureki kibaridai ki kammala karatunki tukum ...

Ajiyar zuciya zeenat tayi tace ALLAH mom ?"

Mom tace kwarai kuwa,Kinga byn kin auresa sai musan y....salamu alaikum cewar Hafiz dake ta sallama su mom basujiba...

Da sauri mom ta d'ago taga Hafiz ne,kicin kicin tayi da rai had'e da amsawa fuska bbu yabo bbu fallasa.

Bedamuba da hakan ba sbd  yasaba ,Kuma duk yaji maganarsu,cikin tuhuma mom tace oh wai tun dazu ne kaketa sallama ko yanxun?"

Murmushi yyi yace ah ah shigowa ta kenan  Ina wuni mom?" Yacanza topic d'in,amsawa tayi bata kallesaba.

Yadubi xeenat Yana murmushi yace madam ya kk ?AK nanan?"

Mom ta karbe zancen da cewa 
Cikin bada order  eh amma nahana kowa ganinsa yanxun...

Murmushi Hafiz yyi yace to shikenan mom na wuce"

Kagaida gd,ya girgiza Kai yafice ,mom tarakasa d harara.

Sannan suka cigaba da fira da zeenat.

Bangaren harira kuwa tunani ta hauyi byn ta bar gdn hjy hafsatu wato mom akan wata samoma mom.

Kwatsam riyanatu ta fado Mata arai ,afili tace to ALLAH yasa uwarta ta amince Dan nakura yarinyar akwai hankali d nutsuwa.

Ay tuni harira ta nufi gdn zuwaira mai abinci.

Sallama tayi atsakar gd tasamu su riyanatu da Fatima suna ta fira yyinda umma d zuwaira keta aikin yin miyar abincin siyarwa.

Gaisawa sukayi sannan harira ta bukaci ,su riyanatu subasu guri suyi mgn ,bbu musu su bar gun.

Sannan harira ta Fara dubar zuwaira tace dama wata damace tasamu ,shine nace baranaxo gurunku.

Zuwaira tace to munjinki"

Harira tace kinsan Alh KABIR GIRMA ?"

Zuwaira tace kwarai kuwa"harira ta koramusu bayani game d bukatar mom , sannan tace to aganina in har yarinyar nan zata iya me zai Hana muje da ita ,agayamata abinda zatayi abiyata salin alin Kuma abinda yasa nace haka gsky yaron kirkine bbu wata matsala Dan ko mgn Bata damesaba balle yakalli mace.

Shin yakuka gani Dan wlh zata samu albashi mai tsoka sosai .

Zuwaira tadubi umma tace to yakikagani ne yanzun.

Umma tayi ajiyar zuciya tace.....


Share pls 


BY MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
  mmn fareesa


Wannan shafin nakine mmn sultan aminiyar k'warai.๐Ÿ˜marubuciyar SON ZUCIYA kiyi yadda kikeso dashi Ina mugun jidke๐Ÿ˜‡๐Ÿ˜‡

Jin jina ga 
ZUMUNTA novels
MMN SHUKRA novels
AUREN WATA SHIDDA novels 
Maimuna..
Bilkisu Auwal
Queen
Teema
Aysha k y 
Mmn arfart
Hanifa isah k
Zee hamis wada
Inajin dadin comments naku sbd ku nayi typing kuna dabanne azuciyar mmn fareesa๐Ÿ‘๐Ÿป❤

Mmn fareesa fans page&auran wata shidda fans ku gyara bakwasan comment zandena posting daku.๐Ÿ˜œ


P5

.....Umma tayi ajiyar zuciya ta kalli zuwaira tace kiramun mariya awaya muji me zatace inta amince to nima na amince.
     Zuwaira tace to shikenan,nan takira number gali tasanardashi tanason mgn da Inna mariya,yace to bara yakai Mata wayar baya gd.
befi minti3 ba da yanke wayar yakira, umma ta daga had'e da yin sallama"
Cikin murna suka gaisa da Inna mariya da tambayar su bbu matsala daiko ?"
Umma tace eh, sannan tasanar da ita mgnar aikin da riyanatu zataje.
Inna mariya tace to ai bbu matsala bintu tunda bama aikatau bane Dan aiki neba waniba,amma gsky kiyi Mata fad'a ta rik'e mutuncinta da Kuma gsky dukda nasan halin riyanatu yarinyace. Nutsatstsa amma ki tunarda ita.
ALLAH yasa hakan shiyafi alkhairi"
Umma tace ameen"
Inna mariya tace dama kuwa gobe nikeso Zan turo gali yakamiki kudin tumakinki dubu15 kunyi amfani dasu sannan ki siyawa riyanatu Yan kaya tunda ance gdn masu haline.
Umma tace to ALLAH yakawosa lfy.inna mariya tace ameen ,Wai kinsan byn tafiyarku kuwa yadda Iro da baffan riyanatu sule sukatashi hankalinsu,saida naje har gd namusu bayani tukum hankalinsu ya kwanta ,Kuma iro yace insha ALLAH zaizo yarika dubaku tunda ya rasa Yaya HAJARA kema bazaiyi sakaci yarasaki ba...hawaye yazubowa umma sbd jin an anbaci HAJARA  y'ar uwarta wadda batasan araye take ko a mace ba....cikin Jan majina tace to ngd sosai agaishe dasu,Koda inna mariya taji muryar umma tasan kuka tayi sbd jin sunan HAJARA.nan sukayi sallama,,,

Zuwaira tayi ajiyar zuciya sbd ganin umma na goge hawaye tace kiyi hkri dukda bansan miyasa kikekukaba,Amma yakukayi d ita?"


Umma tace bbu matsala duk mun amince, sannan ta dubi harira dake kallon su tana washe baki jin sun amince tace to yaushe zata Fara be?"

Harira tace eh yanxun gobe Zan zo muje gdn zaa sanar da ita aikinta da lokacin zuwa da albashinta, sannan afadi ranar dazata Fara.

Umma tace to ALLAH yasa hakan shiyafi alkhairi"

"Zuwaira tace ameen"

Sannan sukayi sallama da harira.

Umma ta k'walawa riyanatu Kira....da sauri ta fito dg parlourn mama zuwaira, kallon ta tayi had'e da Kiran sunanta ,hakan yasa riyanatu gane cewa  maganar da umma zatamata mai mahimmanci ce,sai ta amsa anutse"
Sannan umma ta Mata bayani komai game da aikin da zata Fara...
Atsorace cikin jin faduwar gaba tace aiki Kuma umma?"sannan nmj Wanda bansan halinsaba nidai gsky...sai Kuma tayi shiru... murmushi umma tayi sbd yasan abinda riyanatu kesan fad'a be wuce tace tanajin tsoro ba sbd abinda yarima HAMZA yaso yima"
Ahankali umma btace duk abinda zakiyi arayuwa kiyi da zuciya d'aya, sannan kada kisaka zargi aranki ko zato sbd mafi akasarin zato karyane riyanatu Kuma baduka aka Zama dayaba ,duk lalacewar duniya da mutane baza a rasa mutanan kirkiba sbd ni inaji ajikina wannan aikin da zakiyi alkhairi ne ko yanxun ko nan gaba , sannan Kuma bawai Ina nufin ki dauwamaba da yinsa aha ah!,insha ALLAH abinda kikasamu inkin yi Yan watanni dashi zamu nemi wata sanaar kibar aikin insha ALLAH..


      Ajiyar zuciya riyanatu tayi sbd ta gamsu da zancen umman ta, sannan Kuma mama zuwaira ta kara Mata nasiha.....

    #####

Washe gari harira ta Kira hjy hafsat tasanar da ita anjima suna nan tafe da yarinyar ,mom tace to sukayi sallama, sannan takira abdallah taji wayarsa busy .sai byn kusan minti25 ta kirasa tace yazo parlourn ta yanxun,kasan cewar Yana gd.

Sallama yyi hade da Zama kuda ita,yarik'e hannunta Yana murmushi had'e da cewa my sweet mom gani"
     Fuska bbu walwala tace my son dawa kake waya?" naji wayarka is carry busy... murmushi yyi yace wlh mom abbane gsky Abba yadawo haka nan cikin familyn sa ....yatsina fuska tayi had'e da cewa dallah rufemin baki tunda gani ai ba wani Abu bane ko?" shiru Abdallah yyi Yana mamakin halin mom....katsesa tayi da cewa yau my son kaga yau Friday ko?"to insha ALLAH me kula dakai dg Monday zata Fara aikinta yau ma zaa kata muyi mgn"
Fuska bbu yabo bbu fallasa ya ce ok had'e da tashi da nufin tafiya.
Mom tace sai Ina Kuma?" Yace zanje gun hafis ne,! Yauwa mom jiya miyasa kika hanashi shiga guna pls ya marairaice fuska?"
Fuska daure tace to ubanah k'arata yakai gunka neka hukuntani kome?"
    To nahana sbd na isa ne...cikin girmama wa Abdallah yalangabe Kai yace kiyi hkri mom bansan mgn ta zata Bata Miki raiba , yafad'a had'e da dawowa ya aza kansa akan cinyarta.
Shafa kansa tayi tace shikenan my son nahakura Amma kadena fadawa hafis sirrinka kaji?"Abdallah yace to, sannan suka cigaba da fira.;;;;


Da misalin karfe 2:30pm mai adaidaita yasauke harira d riyanatu a kofar gidan alh kabir girma,byn sun sallamesa suka nufi k'atan get d'in gdn da riyanatu tashagala d kallo wani gefe na zuciyar najin faduwar gaba had'e da tsoro.

Get man ne yazo yabude karamar kofar shiga ,Koda yaga harira bbu musu yabasu hanya sbd yasanta ta Saba zuwa gdn.

Harira ta kalli riyanatu tace to yannan ki kama kanki kinjiko kada ki nuna kinada wayo kinji?" riyanatu tace to hade da mamakin miyasa harira tace haka.

Tafiya sukayi mai Dan nisa, yyinda riyanatu ke yaba kyawun gdn a zuciyarta,har suka iso kofar da zata sadaka da babban parlourn gdn.

Sallama sukayi kafin su shige ciki,bbu abinda ketashi a parlourn sai kamshin room frishners da turarukan wuta sai sanyin AC.

Masu aikine keta Kai da kawowa ,su suka amsa sallamar su, sannan byn sun gaisa harira ta bukaci suyi Mata mgn da hjy ...

Sunkai kusan minti20 zaune har zaman ya ishi riyanatu ta Kuma tabbatar matar gdn batasan darajar bak'o ba.. maganar mom ce da kamshin turarenta yadawo da ita tunanin ta d'ago kanta da sauri sukuyi 4eyes da mom ,suduka atare gabansu yafadi, yyinda riyanatu ta sunkuyar dakanta k'asa.

Cikin yatsina had'e da izza mom tace wannan itace yarinyar?" Ta fad'a cikin gadara fuska bbu walwala, yyinda wani b'angaren zuciyarta ta tsorata da kyawun yarinyar.

Harira tace eh"

Riyanatu ta yi saurin dukawa tace hjy Ina wuni?"

Lfy ,ta amsa atakaice"had'e da cewa to da farko dai inason ki bud'e kunnanki kijini da kyau game da aikin da zakiyi .

Cikin girmama riyanatu ta ce to"

Mom tace da farko dai ranar monday Zaki Fara aikinki,kitabbata karfe7am tamiki agdn nan,sbd my son karfe8:am yake tashi to kafin yatshi kin gyara masa parlourn sakin wanke Masa toilet kin hada Masa ruwan wanka.

Inyashiga wanka ki gyara bed room d'in sa,kafin kije kitchen gun kuku ki karbo Masa break fast nasa kiyi serving nasa, sannan ki gyara Gurin da Kuma sake gyara bed room nasa sbd bayason k'azanta shi mai tsabtane sosai Dan in har bakida tsabta zaku Bata dashi gsky fuk in kika gama zuwa 9 am Zaki iya tafiya musammun inkina skul ,sai 2:pm kidawo sbd 2:30yake shigowa yyi wanka yaci abinci ,Zaki cigaba da kulawa dashi har4:00 pm sbd Yana fita Kinga inkina islamiya sai kije dg nan ki wuce gd sai wata safiyar.

dg karshe my son bayason surutu had'e da shishshigi,nima haka, sannan ban hada Dana da kowaba muddin ki ka b'ata Masa rai can hukuntaki nakuma koreki , sannan kada ki yi zaton d'ana mutumin banzane kice Zaki ja raayinsa da kyawunki to ba haka ABDALLAH yakeba.nasake gayamiki ki kularmun da yaro kada ki bata Masa rai....

Jikin riyanatu yyi sanyi,jiki bbu lakka tace to insha ALLAH Zan kiyaye.

Harira tace ai hjy batada matsala yarinyar nan....ban tambayekiba ,mom ta katse harira hade da zuge jaka ta fito da kudi ta mik'awa harira , sannan tace albashin ta a wata dubu 30 be,sai Monday din.


Harira ta karba , sannan tayi godiya , sannan tace ai hjy anyi hutun boko itakuma sai islamiyya take,mom tace bbu damuwa akwai islamiya farkon layin nan zanma ya'u  direba mgn asiya Mata foam intazo saita ruk'a zuwa.

Godiya su riyanatu da harira sukayi kafin suyi sallama su fice,mom tabi bayansu da harara.


Koda suka fita , adaidaita suka hau ,har gd harira ta raka riyanatu ta ma su umma bayanin komai da irin aikin da riyanatu zatayi da albashinta da sakata islamiya duk sunji Dadi sosai , sannan harira ta dubi zuwaira tace ammainaganin kafin Monday din yaka Mata akoya Mata kamar...
Wanke bayi da yadda ake hada ruwan wanka da turare d'aki dasu moping da sauransu dukda nasan xata iya amma gara ak'ara nuna gudun kuskure ..

Zuwaira tace to shikenan Zan saka Fatima suje gdnsu yusra kawarta tunda suma masu haline sai ta kara ganin yadda ake amfani da komai .

Harira tace to sannan suka yi sallama.

A cikin kwanaki biyu  riyanatu ta koyi duk abinda akeson ta koya, yyinda riyanatu ke ta faman Yaya zata kasance da ita gobe Monday agdn aikinta.


Monday....
   
Innaga ruwan comments kujini da safe....
      Happy juma at kareem❤

Share pls

BY MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story & written by
   mmn fareesa

Dedicate to all my fans ana mugun tare๐Ÿ˜๐Ÿ˜„

p6
     
          Monday

    """"Tun  gurin karfe 6:30 riyanatu ta shirya cikin doguwar riga bak'a y'ar kanti tasaka hijab Fara "bbu wata kwalliyar datayi dg powder sai kwalli ta shafa ,sukayi sallama da umma dasu Fatima dake Mata fatan alkhairi itada mama zuwaira"

Adedeta tahau ,ya ajeta a unguwar nassarawa G R A.byn ta sallamesa tashiga ciki kasancewar get man yasan da zuwanta.
     Waiting parlourn gidan ta nufa gabanta na mugun faduwa,tasami mom da Yan aiki"har k'asa ta tsugunna ta gaishe d mom ,ta amfa fuska a tamke yyinda tasaka ladidi(d'aya dg cikin masu aiki) ta nunawa riyanatu part d'in Abdallah..,,,

       Suna zuwa kofar shiga part d'in ladidi ta juya ta tafi"
Wani mugun tsorone fal aranta ,amma saitayi jarumta had'e da yin addua azuciyarta,kafin ta murd'a kofar tayi sallama"bbu kowa a parlourn"
Tasbihi riyanatu tayi da ganin wannan kayataccen parlourn a zuciyarta ,ko Ina k'al amma Wai nan sai an gyara sai kamshi ketashi na room frishners aciki..
Kofar dake cikin  parlourn ta kalla hakan yanuna Mata nan be bed room d'in.
Tsintsiyar data shigo da ita had'e da mofa da wani towel ,tasaka ta Fara gyaran parlourn had'e da karkad'e kujerin d kayan kallo , sannan tayi moping.
Ta duba taga komai yyi daidai.
Sannan ta nufi kofar bed room gabanta na dukan Tara Tara,tayi Knocking yafi sau 3 shiru hakan yasa ta murd'a kofar tashiga ciki ahankali had'e da yin sallama,amma shiru"bed d'in tasaci kallo ta hango mutum kwance atsakkiyar yarufe jikinsa d alama bacci yake.
Kofar dake da keda carpet takalla ganin harda silifas akan carpet din haka yatabbatar Mata da nan ne toilet..

Addua tayi ta shige  ciki " sai zare ido take sbd atsorace take,Saida ta k'arewa toilet din kallo tukum sannan ta Fara aikinta , azuciyarta tana  mamakin Wai bayine wannan aka zubawa kayan alatu haka tamkar baza a mutuba , lallai mutumin nan d'angatane sannan akwai muguwar tsabta gsky....
da wannan tunanin ta gyare toilet din k'al har tayis d'in jikin bango Saida ta wanke , sannan ta wanke hannunta ta fito.....tana fitowa taga mutum tsaye gaban mirro dg shi sai towel iya guiwa da alama wanka zai shiga ,yabada baya hakan yasa bataga fuskarsaba..
Ta tsorata ainun takuma razana sbd batatab'a ganin nmj hakaba "da sauri ta d'auke kanta had'e da cewa  ranka yadad'e Ina kwana?" har sau2 jin yyi Mata banza sai ta nufi Gurin bed Dan ta gyara.
Shikuwa Abdallah uffan beceba Kuma be kalleta ba yawuce toilet ya rufe,k'arar rufe kofar ya ankarar da ita baya cikin room d'in"
Ajiyar zuciya tayi azuciyarta tace oh ikon ALLAH lallai mutumin nan baisan darajan d'an adam ba ...


Cikin minti 25 tayiwa bed room d'in fas,ta duba kan mirro ta dauki air freshener ta feshe ko Ina harda parlourn tuni guri yakaure da k'amshi..
Bed room d'in ta koma ta ajiye air freshener din sannan ta duba wardrobe din haggu cikin saa taga bed sheet da sauri ta dauka ta canza ,sbd Fatima ta Bata shawarar ta rik'a canzawa tunda ance shi mai tsabtane.
Wayoyinsa data aza kan mirror taje da nufin ta dauka ta mayar Masa kan bed inda tagani... adedenan taji motsin zai fito da sauri ta janye hannunta ta nufi kofar fita dg bed room d'in...

Waye zai fitomiki da kayan da Zan saka?"

Yafad'a cikin husky voice,tamkarbashi yyi maganarba" 

Cak yatsaya hade d juyowa sukayi 4eyes dashi"Masha ALLAH tace azuciyarta sbd ganin baiwar halitta agun sa,tayi mamakin jin  yyi hausa ,dabaiyi mgn ba saitace balarabene bayajin hausa....tsakin dayajane yasata janye idanunta dg barin kallosa.

"Ahankali tace Ina kayan suke?"

Tasake tambayarsa, yyinda shikuma yaketa duba body cream nasa  ,yamata banxa...d hannu yanuna wardrobe d'in tsakkiya"
azuciyarta tace oh ni nashiga3 ,Toni nasan irin kayan dazai sakane?"

Jiki bbu kwari ta nufi wardrobe d'in ta bud'e, lumshe ido tayi sbd jin kamshin da kayan keyi....Saida ta ce Masha ALLAH sbd ganin tulin kayan sawarsa duk yawancinsu k'ananu ne" addua take ALLAH yasa kada tayi ba dai daiba "can idanunta suka hasko Mata wasu suit dark blue da sauri ta fito da su,kasancewar tare suke da wandon da komai ta aza kan bed ta fice da sauri sbd tunawarta da karb'o Masa breakfast..


A babban parlourn gdn ta koma ta Sami mom na break fast a dining area ,ta isa gunta cikin ladabi tace hjy na gama Ina ne kicindin?"

Tsaki mom taja hade da nuna mata wata  kofa da hannu sannan tace kije can ki karba inya gama kije can ki karbi naki sbd ba Wai nasa zakiciba ,abincin masu aiki dabn yake dg yanxun ban abukatar kisake tambayata in 4 tayi kije bakin get gun ya'u direba zai kaiki islamiya ga yunifaom nan ta nuna mata wata leda dake k'asa kusa da kafarta.

Jiki asanyaye ta dauka had'e da yin godiya ta wuce kicin ta karb'o break fast nasata koma part d'in sa.


Da sallama ta shiga ,zaune ta samesa a parlourn yasaka kayan agogo na hannunsa ,gefensa takalmi sawuciki kafarsa d safa.

Gun dinning ta nufa "ahankali yace kawo nan yafad'a Yana latsa waya"ajiyewa tayi ,ta mik'e da nufin tafiya....waya Baki izinin tafiya?"

Juyowa tayi ta kallesa,fuska daure yace last warning dazan Miki game da kallona"yafad'a had'e da mik'a Mata agogon sa "

Da mamaki t karb'a tana dubawa ,sai Kuma taga ya Miko Mata hannunsa na dama danufin ta d'aura masa"cikin tsoro da mamaki tace Dan ALLAH banganeba ?" Kuma kayi hakuri innayi badaida  b kada kafad'awa hjy sbd tace Inna maka laifi korata zatayi..... stop it yakatseta atsawace had'e da cewa surutu kikazo kimun ko aiki?"

Da sauri tace aiki"

Tsaki yaja had'e da saka takalminsa,yasake mik'a Mata hannu alamar tabasa agogon sa"cikin muryar kuka tace
Kayi hakuri me zanyi d agogon?"

Tamkar mai koyan mgn yace ki dauramun....

Zaro ido tayi tace....


Muhadu da marece pls kuyi manage da wannan๐Ÿ™๐Ÿป

Share pls

BY 
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
    mmn fareesa

Wannan page din nakune halak malak AUREN WATA SHIDDA FANS &mmn fareesa fans page Ina mugun jidaku bbu laifi kunyi comments๐Ÿ˜๐Ÿ˜‡

p7

.....Zaro ido tayi tace ai ban iyaba!kayi hakuri Dan ALLAH"banza yyi da ita yasake mik'a hannu da nufin  karba"zabura tayi had'e da sakin agogon k'asa tana hawaye had'e da cewa kayi hakur....are you mental?" Yafad'a atsawace had'e da mik'ewa tsaye yadauki agogon sa had'e da dubawa kota kashe Masa glass d'in"
Saka abinsa yyi  ganin baiyi komaiba"Saida yagama Shan k'amshinsa , sannan yace serve me break fast yafad'a batare da yakalleta ba"
     Ita kuwa hawaye kawai take jin yace ita Wai mahaukaciyace , sannan Kuma dayace tayi serving nasa batafahimci me yace sbd(kunsan skul din kauye bbu wani karatu)
Cikin muryar tace ranka yadad'e nifa ban f.....I say don't call me ranka yadad'e,call me ABDALLAH!
Ni bana fahimtar turancin kayi mgn da hausa manah.... tsaki yaja ganin wannan yarinyace k'arama,yadago Kai yaga tana kuka wata uwar harara ya aiko mata da ita. cikin bada order yace kixo ki hadamun tea da sauran kayan , sannan kika sake mun kuka anan Zan nuna Miki calour d'ina yafad'a Yana yatsina fuska"
     Tashi tayi , zuciyarta bbu Dadi ganin wannan mai girman kan na juyata kamar bewarsa duk sai taji aikin yafita aranta ,zata jurene kawai sbd umma.,,,,

     Haka ta daure ta hada Masa tea din tana d'ar d'ar , sannan Bata cika suga ba sbd gudun laifi,amma tayiwa cup din dam da tea, sannan tasa Masa chieps ta hade da farfesun kaji๐Ÿคฃ

d'auka tayi ta aje gabansa , had'e da cewa ranka yadad'e gashi... adedenan Hafiz yyi sallama yashigo cikin parlourn, riyanatu ta amsa had'e da cewa Ina kwana?" ganin yanata kallonta"sannan ta mik'e da nufin fita.hafix Yadubi Abdallah yace AK duk Kai daya zakaci wannan garar? da sauri Yadubi plate d cup din....
    Keeeeee! I don't go"Abdallah yafad'a rai bace ganin kwabar da tamasa na hade chieps d farfesun kaji gu d'aya...cak ta tsaya had'e da juyowa taga yyo kanta ! saurin toshe bakinta tayi sbd kukan daya taso Mata azuciyarta tace naga ta kaina"
 Sai zare ido take....d sauri Hafiz ya danne dariyarsa yarik'e hannun Abdallah had'e da cewa calm down abokina!kaga ka tsorata ta ,pls kayi hakuri...
Tsaki abdallah yaja had'e da nuna riyanatu yace you are very stupid! sannan ya fisge hannu sa dg na hafis Yadubi riyanatu dake kuka yace dama ciwon Kai kikazo kisamun b aiki kikazo yiba get out of my parlour"yafad'a atsawace....
      Hafiz ta kallah fuska kalar tausayi tace Dan ALLAH kabasa hakuri ,hjy tace dana Masa laifi korata zatay....bazaki fitaba?" Cewar Abdallah batare da yakalleta ba.

Hafit  yace jeki bbu komai kinji,bazaa kore kiba!

Jiki asanyaye ta fice"

Abdallah ya ya tsina fuska had'e da cewa Kai mlm dakace baza a koreta ba, Kai zata bi ko saita ruk'a maka ko?

Hafiz yyi murmushi yace Wai mutumin wannan fine baby dinfa dg Ina?" Kai gsky ta had'u akwai kyau tamkar aljana ai wlh I.....dallah mlm ya isa haka sai zuba kake bbu commer balle full stop,cewar Abdallah .
Yana tsaki.

Murmushi Hafiz yyi yace eh naji ka amsamun tambayata.

Saida yagama Shan k'amshinsa sannan yace mai kula danice !amma dg yau kuma zatabar aikinta ,sbd bata iyaba . kaduba kaga  wannan haukan datamun... relax Mana AK ,kaga yarinya ce sai ahankali zakaga yadda kakeso, sannan na lura tana tsoronka Dan ALLAH kabita ahankali saikasa mom ta nuna mata inda tayi kuskure saita gyara amma pls kada ka koreta sbd naga batason akoreta.
Kuma tunda ta Fara aikinta duka duk ba daidai tayiba ko kuwa yanxun tayine b daidaiba?"
Yatsina fuska yyi hade da cewa babu laifi tayimun gyaran daki yyi"
Hafiz yace  to pls maganar korarta ka ajiyeta gefe,sanny kada ka gayawa mom sbd na lura tana tsoronta itama.

Ok kawai Abdallah yace atakaice, sannan ya hada tea ,yyi serving kansa .

Shima Hafiz haka"
Sai Gurin 9:14 am suka fito da nufin Abdallah yaje yagaishe da mom.

Suna fitowa suka ganta zaune tayi tagumi idanuwa sunyi jajir alamar taci kuka"
Cikin tausayawa Hafiz yace kaga kasaka bewar ALLAH damuwa k... kallon da Abdallah yyi Masa ne yasaka shi yin shiru Yana murmushi .

      Da hannu Hafiz yyi Mata alamar ta biyosu,da sauri kuwa ta taho ,tana satar kallon Abdallah caraf suka hada ido yabanko Mata harara had'e da miko Mata wayoyin hannunsa Yana Jan tsaki.
"Karba tayi tabisu a baya har suka iso part d'in mom"
aikoda mom ta gansu tuni ta had'e rai aciki ciki ta amsa gaisuwar Hafiz, sannan ta watsowa riyanatu mugun kallo had'e da cewa kefa lfy Zaki wani kwaso jiki ki biyosa?"shin tamayi komai yadda yadace ko kuwa tayi wani gidadancin ?""

Girgiza Kai Abdallah yyi alamar ah ah"

Kallon su tayi had'e da cewa to kuban waje nayi mgn da yarona ko"

Murmushi Hafiz yyi yace to momi, sannan Yadubi riyanatu yace muje ko" bbu musu ta bisa suka fice"

Hanyar part d'in Abdallah Hafiz ya nufa hakan yasa tabisa,ahanya yace kiyi hkri kinji meye sunanki?"

Tace RIYANATU"

Yace ok ,muje na nuna Miki inyace kiyi serving nasa abinci ,sai kiyi Masa.
Murmushi tayi tace nagode sosai.
Shima murmushn yyi da haka suka isa part d'in.
Tea yafara hadawa  yadda yasan abdallah naso ,yace ta sha , sannan yyi serving aplate da sauran abinda suka rage, sannan yace Mike baki ganeba?"
      Shiru tayi sannan ta ce inyayi mgn da turanci wani lokacin bani ganewa"murmushi yyi yace ko Zaki iya tunakal mar daya fad'a bakiganeba?"
Cikin jin kunya ta fad'a Masa, y'ar dariya yyi yace cewa yyi kidena kiransa da ranka yadad'e ki rik'a kiransa da Abdallah"

Ahankali tace to amma injin nauyin Kiran sunansa Kai tsaye..... ringing d'in wayarsa ta katse Masu mgn,da sauri ta shi da nufin Kai Masa.
Hafis kuwa yace Kinga kijirasa zaizo tunda mom tace mu basu waje,nima na wuce inyazo ki fad'a masa.

Bata kallesaba tace to shikenan nagode, murmushi yyi yace pls kici abincin nan kinji sbd ya koshi karshe ma badashi zaayi....da sauri ta ce ai hjy tace kada na ci ,naje can na karb'o acikin na masu aikin gdn.

Shiru Hafiz yyi,Yana tunanin hali irin na mom,sbd gudun kada ta disgata yace kada takai wayar"Kai Anya matar nan akwai gsky alamarinta?"

Kallon riyanatu yyi yace ki ciki kinji inkin gama ki Kai kayan gun masu wanke wanke ,baza tasan kinciba sbd in ya rage abinci masu gadi yake ba.
bejira amsarta ba yafice dg parlourn.

Ita kuwa riyanatu bbu bata lokaci taci ta koshi ta gyara parlourn tas , sannan ta fito da kayan da sukayi break ta nufi part din ma'aikatan gdn,ta tambayi gun masu wanke wanke aka nuna Mata takai masu.

Komawa tayi part d'in Abdallah,da nufin dauko Masa wayarsa ta Kai Masa,tasamesa zaune hakimce kan 2 seeter yana latsa waya, sallama tayi ...ya amsa akan labb'ansa "
Ahankali tace dama zantafi gd!
banza yyi da ita dg karshe ma sai ya rufe ido "tab'e Baki tayi had'e da dage kafad'a alamar ko ajikinta "saidai batasan duk Yana kallon ta ba"hijab nata ta gyara ta nufi kofa da nufin fita....keeeeeee!cak ta tsaya cikin k'uluwa ganin raininwayonsa yyi yawa besan tana d'aga masababa"tagaji haka nan,shiru tayi ita batayi mgn ba ,Bata Kuma juyoba" yyinda shima yyi shiru.takuma yi alkawari muddin bazaiyi mgn ba to itama bazatayi ba saidai sudauwama a haka .

Shikuwa gogan yacika yyi fam da rainin hankalin wannan ta tsitsiyar yarinyar nan,wani gefe Kuma Yana tunanin magan ganun mom na d'azun byn tafiyar su Hafiz,yarasa me Hafiz yakashewa mom, sannan miyasa batadamu da Abbansa yadawo gd ba koma maganar sa bataso yyi shin Wai Mike faruwa ne haka ?""
      Sake duban riyanatu yyi dake tsaye tun d'azun databashi baya ,tsaki yyi azuciyarsa yace me wannan tsakuwar yarinyar nan ke nufi?" wato ita bazatayi mgn ba kenan ,aiko in har sainayi mgn zata yi to saidai ta kwana anan,kuma ta tafi to bakin aikinta.....

Riyanatu kuwa...

Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by 
Mmn fareesa
 

Not edited

p8

"""Riyanatu kuwa gajiya tayi da tsayuwa "sotake ta ta fi gd "tana gudun kada ta tafi yakoreta.azuciyarta  tace bara na kyalesa kawai "cikin jin haushi ta juyo tana murgud'a baki tace Dan ALLAH kasanar dani me zanyi ?" 
     banza yyi Mata ,Kuma Yana lura da murgud'a bakin datayi"sai da yagama Shan k'amshinsa tukum "ya ware golden eyes nasa akan fuskarta "ya had'e girar sama d k'asa"saurin janye idanunta tayi sbd jin yyi Mata mugun kwarjini....mitttsss yaja tsaki hade da cewa ke vileger girl wakika bari yagyara Miki bed room d'in?"
and last kika koma kallo na ko yimun mgn atsatstsaye amatsayinki na hadimata to Zan koyamiki manner of toking"maana ladibban mgn dan nalura da alama kinada k'wak'walwar kifi.... mitss yakoma Jan tsaki akaro na biyu sannan yadauki wayoyinsa yafice had'e da buga kofar  da k'arfi....
Hawaye masu zafine suka wanke Mata kunci sbd jin haushin abinda yyi mata....oh dama haka masu aiki ke ganin irin wannan tozarcin?"lalai dole ma tabar gdn duk rintsi ,amma bazata gayawa umma komaiba kodan sbd kada taji haushi ko hankalinta yatashi... ajiyar zuciya tayi sannan ta wuce ciki tasake gyarawa tukum ta fito ta nufi part d'in mom ...

     Ladidi ta gani a waiting parlou tace Ina hjy Dan ALLAH?"
Tace tana parlourn ta,Kinga kofar can ta nuna mata da hannu"kofar ta nufa ta murd'a....cak ta tsaya sbd jin wasu maganganu da kus kus....innalillahi wa inna ilaihir Raju un kawai Riyanatu ke maimaitawa azuciyarta had'e da saurin toshe bakinta"sbd gudun kada aji motsinta "ahankali ta ja kofar had'e da yowa baya jiki na b'ari tabar part d'in..
Tunani take azuciyarta shin Wai meke faruwa ne?" Ita Tama fasa zuwa gd bara kawai tabari sai 6 d'in kawai tunda sai taje islamiyya"guri tasamu a gurin flawas na gdn tayi ta gumi tana kuka shin Wai wannan wace irin masiface ne?" Itadai rabon wahala yakata gdn nan da yanzun suna garinsu Kai ita dai tsakaninta da yarima ALLAH ya isa sbd shine sanadin zuwanta garin nan"
Ajiyar zuciya tayi had'e da d'aga Kai sbd wani tunani dayazo Mata dukda atsorace take.

    Tafi awa1 anan har kusan 12: sannan ta bar Gurin ta tafi gab da part d'in Abdallah ta tsaya" batafi minti12 ba ta hangosa da body guards nasa suna biye dashi har suka iso gab da ita da sauri ta tashi tsaye had'e da satar kallon Abdallah tag a fuskarsa atamke"suit d'in dake rataye kan kafad'arsa tasa hannunta ahankali ta janye had'e da binsa ciki"ganin ya sallami guards nasa.


Suna shiga parlou yace zanyi wanka"atakaice sannan yashige bed room d'in beko kalleta"girgiza Kai tayi tabi bayansa"
      Toilet ta wuce ta had'a Masa ruwan wanka tana mamakin Wai baya gajiya da yin wanka dudu ba gurin8 yyiba amma gashi yanxun be fi 12:30 ba Amma zai sake"
 Fitowa tayi tace ranka yad...am in ab... mitttsss yaja doguwar tsuka had'e da tashi Yana kokarin cire kayansa "yyinda riyanatu tuni ta fice.

Tana komawa parlourn "xeenat nayin sallama suka had'a ido da riyanatu...wani faduwar gaba xeenat taji,murya asark'e ta kalli riyanatu up& down tace WHO ARE U?"

Tab'e Baki riyanatu tayi had'e da Zama kan kujera...da sauri zeenat tace keeeeee y'ar matsiyata ,talaka uwar me yakaiki dakin mijina ne ?"iye bazakiyi mgn ba Dan ubanki?"

Ak'ule riyanatu tace ya isa kinzo inda bazan iya jurewa sbd banhad'a iyayena d kowaba ,kada ki koma zaginsu, sannan dakike cewa mijinki ai Ni banga alamar ke matar aure bace ajikinki sbd duk macen datasan darajan kanta bazata yi shigar d kikayi ba.....ke wawiya y'ar iska mikikaje kukayine da kika fito da bed room d'in sa?"zeenat ta fad'a tana huci had'e da d'aga hannu da nufin Marin riyanatu.

Da sauri riyanatu ta rik'e hannun had'e da cewa baki isaba! sbd banmiki komaiba...afusace zeenat na fisge hannunta ta nufi bed room d'in tana cewa inke baki fad'a ba shi dole yafad'a mun...
Turus zeenat tayi sbd ganin Abdallah gaban mirro tsaye sg shi sai towel...shi kuwa jin anshigo ya zata riyanatu kasancewar yabada baya,cikin bada order yace ki fitomin da kayan....whattttttt?" Abdallah me kake fad'a haka ?"kaddai ace yarinyar nan.... afusace yajuyo sbd jin muryar zeenat"cikin tsanar halayenta yace lfy malama ?wabaki izinin shigomun bed room?" 
A k'ule zeenat tace bansaniba Abdallah dama Kai maciyin Amana ne bansaniba to wlh kasheta Zan yi.....ta fad'a tana kuka hade d ficewa...
Tuni ran Abdallah yyi mugun b'aci dan in ya fahimci zeenat tana nufin sun aikata Masha a da wannan y'ar k'auyen kome?"
afusace yajawo jallabiya yasaka yafice dg bed room d'in.,,,

Yana zuwa yasami zeenat na dukan riyanatu ta haye saman ta...wasu maruka masu rai d kafiya yabawa zeenat har sau2 ,cikin b'acin rai yace i hate u zeenat nikike ma sharrin zina da mai aikina har kina dukanta sbd ni... girgiza Kai yyi had'e da fincikota yyi wurgi da ita kanta yabigi kujera"ya kalleta da jajayen idanunsa dasukayi ja sbd bacin rai ,yace dg yau kada ki koma zuwa guna na tsaneki bana son ganinki....ya fad'a had'e da sake nufarta....juyowa yyi sbd jin anrike Masa hannu"ido 4 sukayi da Hafiz Yana girgiza Masa Kai alamar yabari"

Zeenat kuwa kuka take tana cewa saita kashe riyanatu, yyinda riyanatu duk ta kara tsorata da lamarin gdn sai kuka take"
     Abdallah ya matsa kusa da riyanatu ya yyimata alamar ta tashi zaune bbu musu ta tashi.... zeenat na ganin haka ta tashi  da gudu ta fice.

Cikin takaici Abdallah Yadubi Hafiz  yace friend katafi kawai nasan gun mom zataje so banason surutu kema Zaki iya tafiya, yafad'a had'e da nuna riyanatu.

Ajiyar zuciya Hafiz yyi yace Ni bara na tafi in ka sauka dg dokin zuciyar kafadamun miya faru"ita Kuma ta tsaya sbd kula da Kai..be jira amsarsaba yafice.


Tashi Abdallah yyi batare da yakalli riyanatu ba yace kije sallah"be jira cewarta ba yyi cikin bed room d'in sa.

Ajiyar zuciya tayi had'e tashi ta je part d'in masu aiki tayo Sallah , sannan ta je kicin Dan karb'o Masa abinci sai a kace ai an karbar Masa "da sauri ta nufi part dinsa harda gudu....tana zuwa ta Sami har anyi serving nasa zai Fara cin abincin" da sauri ta buge hannunsa ,abincin yazube kan jikinsa...

Bece Mata komai ba ,hasalima be kalleta ba, atsorace tace kayi hakuri d'azun nashiga kicin d'in in amso abincin shine naga tsaka acikin wannan kwanon,Kuma akicin din bbu kowa sai naje nayi Sallah shine naje na fadawa kukun yace ai ankawo.....d'aga  Mata hannu yyi  Yana yatsina fuska yace kedashi bakusan aikinkuba ,da wani abu yasame ni kece dashi kum.. sallamar mom ce da zeenat ta katsewa Masa mgn.

Amsawa yyi hade da daure fuska tamkar besan menene dariyaba.

Murmushi mom tayi had'e da cewa oh my doghter,ai wannan mai aikinsace yo ko Mata sun kare aduniya me zaiyi d wannan....pls mom kuje kaina na ciwo sannan dg karshe na tsani zeenat.... look Abdallah yak...cewar zeenat sai tayi shiru sbd nunin d mom ta Mata d ido.

Shikuwa Abdallah ficewa yyi dg part d'in ma, yyinda riyanatu tsoro ne fal aranta.

Cikin xare ido mom tace ke muna fuka tashi ki fice kiyi Shirin zuwa islamiya dg can ki wuce gd sai da safe Kuma kin wani tsaremu da k'wala kwalan idanunki....jiki na kirma riyanatu ta fito ta nufi part din masu aiki.....


Riyanatu taje islamiyya bbu wata matsala sbd dama tasan littattafan addini ,basu tasoba sai 6:00 pm dg nan ta wuce gd.

Tana isa tayi sallama,tasami umma d Fatima atsakar gd.
Zama tayi ,suna Mata sannu.

Sannan umma ta dubeta tana murmushi tace to yayadai , babu wata matsala daiko?"

Murmushi tayi ta ce eh umma "bara naje na huta na gajine"

Tana zuwa dakinsu ta kwanta kan katifa ta Fara tunani....


Bangaren Abdallah k...


Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ
๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
    mmn fareesa


Wannan shafin nakune AUREN WATA SHIDDA FANS & ZUMUNTA novels,kuyi yadda kukeso dashi comments naku yafi nakowa๐Ÿฅฐ๐Ÿฅฐ
Ina mugun jidaku irin totally d'in nan...


p9

.....Bangaren Abdallah kuwa zaune yake byn yyi Shirin bacci Yana tunani... yinin ranar cikin bak'in ciki d b'acin rai  yyisa sbd jin zafin abinda zeenat ta Masa. Kuma Wai mom bata damuba ,Wai Mike damun mom ne Wai?" tanason rusa farincikinsa ta gina farin cikin wata "shifa kwata kwata yakasa gane mom ko jiyafa ya bukaci gobe in hafis zayaje kano gun amminsa yabisa dg nan yaje gdn uncle Suraj Amma sai ta hana ,takuma nuna Masa ranta yab'aci...shifa abin na damunsa ace dg dangin uwa har na uba  ba kowa yasani ba ,shin da haka zaya yi zumunci.... mittsss yaja tsaki hade da jawo wayarsa yyi calling Abba....
Sallama Abba yyi Yana dariya yace my son sorry kaji insha ALLAH gobe Ina hanya Zan Kuma zo maka da wani albishir insha ALLAH.
Turo baki yyi tamkar yaro yace haba Abba dan ALLAH kacika alk'wari "wlh Ina kewarka sosai ga mom duk t.... look kasan banason yawan kawo sukan mominka ko?" so abar maganar gobe nafi so kazo d kanka kadaukeni a air port dakaida guards d'ina...
       Jiki asanyaye Abdallah yace to Abba sannan ya yanke wayar had'e da lumshe idonsa Yana mamakin miyasa Abba ke nuna Yana tsoron mom bacin ita batasan darajar sa ba....da wannan tunanin bacci yyi gaba shi.,,,,,,,


     Washe gari tunda wuri riyanatu ta isa gdn"kamar kullum tayi duk abinda tasaba yimasa , sannan ta karb'o break fast ta aje hade da Zama a parlourn, ta na jiran fitowarsa "bata tab'a komai ba sbd gudun laifi dan yanxun tsab tagane halinsa ....
Sai Yan kalle kalle take jin k'amshin turarensa yasata saurin daidata nutsuwarta dantasan yashigo gurin .da sauri tace Ina kwana?" 
Tsaki yaja had'e da Zama ,Saida yaja kusan second 45 sannan yace ki rik'e gaisuwarki banaso,kiyi abinda ke gabanki...
Shiru itama tayi tana sauraronsa batace komai ba ,saidai ta k'udurta aranta bazaa koma na3 ba sbd sau2 kenan tana gaidashi baya amsawa sai bak'ar mgn dayake gay....in baza kiyi abinda yaka wokiba Zaki iya tafiya,ya fad'a cikin sweet voice d'insa...nanma shiru tayi ,ta ta shi ta had'a Masa komai sannan ta  aje gabansa batayi mgn ba ta mik'e da nufin fita ,tana  Dede bakin kofar zata fice....taji muryar sa Yana cewa waya Baki izin tafiya?"

Banza tayi Masa tazo ta zauna ,tana mamakin isa da girman Kai irin nasa saikace wata baiwarsa ,shin kud'i haukane?"itafa gsky tagaji da wannan wulakancin nasu ,shi yyi uwarsa tayi...
Shikuwa Abdallah haushinta yakeji ganin taki mgn ai Tama rainasa kenan...mitttss Yaja tsaki ,Yana cigaba d latsa waya Yana Kuma break...
Be wani ci sosaiba sbd shi bai wani cika cin abinci ba duk da ba laifi tayi serving nasa komai yyi,ture kayan yyi dg gabansa ,fuska daure yace keeeeeee!banza tayi dashi....keeeeeeeeee wlh kikabari na koma kiranki Zaki gane bakida wayo"tashi tayi taje gabansa ta duk'a batayi mgn ba,kin karb'o break?"girgiza Kai yyi atsawace yace keee! be careful wlh " nizaki rik'a wa mgn da body language uwarme yasa Baki mgn?"dolema na sallameki sbd yawan surutu da kike sani....kayi hakuri Dan ALLAH kada ka koreni ,Kuma ban karb'o break dinba....tsaki yaja had'e da kwantar d kansa kan kujera yarufe ido...
Yakai kusan minti2 sannan yace you can go....

Shiru tayi Bata tashiba sbd bata fahinci me yaceba"

Tsaki yaja had'e da cewa Zaki iya tafiya ki karb'o ,kada kidade zakimun aiki, sannan dg yau da 12:00 pm tayi Zaki tsayazan saka akoya Miki turanci" sbd ni na Saba mgn da turanci ke Kuma ba wani ji kikeba ko kuwa kwakwalwarki ce haka bakya fahimta.... murmushi tayi tanajin Dadi sosai sbd tanaso arayuwarta ta ruk'a mgn da turanci"amma nagode sos....banason godiya a tsarina hakan xaisa na fasa...

Girgiza Kai tayi ta fice ta mamakin wane irin haline da Abdallah?"

Komai aka Masa baa Masa gwaninta .....part d'in masu aiki taje byn ta karb'o break taje can tayi ta koshi tukum ta dawo part d'in Abdallah.


Yana nan zaune yadda ta barsa,byn tayi sallama tace na dawo....aina ganki ko?"ga phone's d'ina nan zanyi baccin one hour and 35 minit Kuma ba silent sukeba ,Kuma banaso akirani k'aran yata dani" bance kisata a silent ba dukda ma bakisan miye security dinta ba , so saiki San yadda zakiyi inhar wani ya Kira  natashi bakin aikinki... yafad'a had'e da mik'o Mata wayoyin.

Zaro ido tayi had'e da kallonsa tace Dan ALLAH ni bazan iya ba Kuma ban fahimci me kake nufiba "


Banxa yyi Mata ya aje Mata wayoyin gefenta, sannan yaje y gyara kwanciyarsa kan 3 seater ya rufe ido.... Shiru tayi tana mamakin wannan tsaka mai wuya daya sakata,takai kusan 15 minit azaune .can ta saci kallon sa taga yyi bacci....k'uri ta Masa d ido tana tasbihi sbd ganin kyawunsa yanata bacci hankali kwance ,yarufe ido eye lashes d'in sa tamkar an xana ga sajensa bak'i Kirin yyi kwance lub a fuskarsa ga sallayarsa data yi baki,ta k'ara Masa kyawu....hmmmm k'ila  yanada yawan ibane shiyasa ta fito Masa,ah ah ai ance ita hallittace ko mutum beda yawan ibada tana iya fito Masa ,Kuma masu ibadar sosai taki fito Masu...cewar riyanatu a zuciyarta.;;;;


Kauda kanta tayi sbd tuna warning da yayi Mata akan kallonsa.

Zaman ne da ya isheta itama saita kwanta kan carpet.... bacci yyi gaba d ita, sun jima sosai can wayarsa tayi ringing,atare suka falka sai zare ido riyanatu keyi....shikuwa hannu ya Miko Mata alamar ta Miko Masa wayar.

Da sauri ta basa?"

Dubawa yyi yaga saura 8 minit ya farka...Dan ALLAH kayi h..stop it! yafad'a had'e da d'aga mata hannu yatshi tsaye had'e da cewa kije gd na sallameki sai gobe ....be jira amsarta ya wuce bed room....

Cikin farin ciki ta nufi gd"
Tana shiga d sallama...turus tayi sbd ganin GALI"

Murmushi yyi  ya kafeta d  ido ganin yadda tayi mugun canxawa , ahankali yace riyanatu ki k'araso Mana "


Murmushi tayi ta isa kusadasu ,shida umma dasuke fira da alama  be dad'e da zuwaba"

Ahankali tace Yaya gali Ina wuni?"yasu Inna dasu baffa na?"

Yace duk suna lfy ,suna Kuma gaidake"

Ta ce Ina amsawa, sannan ta kalli umma tace umma nah nadawo"uma tace da wuri haka , riyanatu ta ce eh atakaice sannan ta wuce ciki ta gaida mama zuwaira da gd itada Fatima , sannan ta dawo gun gali ganin umma ta tashi...

Zama tayi suka sake gaisawa sai wani murmushi yake Mata , yyinda riyanatu Bata ma San yanayiba"

Ahankali yace kinsan kuwa abinda yasami yarima kuwa byn tafiyarku ?"

Ware golden eyes nata tayi ta ce meya faru d mugun?"

Bayan tafiyarku da sati2 sai gdn ilu direba sukayi bak'i dg birni,Ashe yaga yarinyar sadda suka shigo garin,shine yasa abita aga nan Masa ina zata shiga ,Ashe matar ma karuwace suna sukaje agarin sai suka biya gdn ilu direba su kwana sbd matarsa y'ar uwarta .
Shine yaje da dare yamata FYAD'E byn yagama take sanar masa tana da cuta mai karya garkuwar jiki wato H I V ....zaro ido riyanatu tayi had'e da cewa subhanallah!,gali yaci gaba da cewa yanxun kowa yasan yanada ita... sannan liman yaje gun sarkin kano yakai k'arar mai gari "zancen danike Miki saura kwana 3 a nad'a sabon me gari,shikuwa yarima Yana gdn yari sbd daaka lissafa yyiwa Yara 15 fyade ,yyima zawara d matan aure...

Girgiza Kai riyanatu tayi tace ALLAH ya kyauta yashiryi masu irin halinsa.

Gali yace ameen"sannan riyanatu ta tashi taje tana ba su zuwaira lbri,ashema  yafad'a ma umma ta sanar da su,sai cewa su mama zuwaira keyi ai hakkin jama a new sunata jajan abun.

Sai Gurin 2:00pm gali yamusu sallama byn yabawa umma kudin ta da Inna mariya tace zaa kawo Mata  na tumakinta ,yatafi gudun kada yyi dare a hanya.
Yaso fadawa riyanatu abinda ke zuciyarsa besamu damaba.

     ######

Abdallah kuwa Yana fitowa dg bed room d'in sa yawuce airport tarar Abba shida guards d'in su....

Cikin farin ciki Abba ya rungume tilon D'ansa guda aduniya Yana murna ,suka shige motocinsu ...


Part d'in mom suka nufa,bbu laifi Abba yasami tarba a gun mom."

Abinci sukaci tare a dining area harda mom,byn sun gama" sannan abba yaje yyi wanka yyi Sallah ya huta.
Sannan yakira Abdallah dan yazo yaji albishir d'in.

Bayan yakirasane mom tashigo ita,ta zauna gefen Abba saiga Abdallah yyi sallama yashigo.

Zama yyi Yana murmushi had'e da cewa yau Abba naji dadin wannan Rana sbd kadawo lfy.

Murmushi Abba yyi yace nagode my son"

Jiya munyi meeting da president nake fad'a Masa akan fannin zane ka kammala karatunka, shine yatambayeni kanada iyali Ni Kuma nace eh,dukba bansan miyasashi tambayarba.

To shine yace zai bud'e maka campany a nan yakuma zabeka akan duka wani gini na maaikatu ko makarantu ka zanashi sannan agina..

Cikin farin ciki mom tace alhmdllh yanxun yaushe zaa bude campany din?"

Da mamaki abdallah ke kallonta,Yana tunanin wane irin sin abin duniya ne da mom Wai?" Ko jira agama mgn batayi.

Dagowa yyi jin Abba yace Amma fa akwai matsala sbd mai girma president yace in yadawo dg k'asar India da 3 weeks za'ayi bikin bud'e campanin atime din angama ginasa to zaiyi kusan 2 weeks acan,shine nike ganin yarinyar nan zeenat d kikeso ya aura ,ayi auran ta ida karatun acan gdnsa ,sbd bazaiyu wu ayi bikin bud'e campanin bashida aureba ,Kuma na amsa yanada aure be kamata yallabai yaga nakasance me mgn 2 ba .

Yaka gani my son?"

Had'e rai mom tayi tace ai zeenat sai taga karatu zai aureta sbd haka acikin 5weeks Zan nema Masa AURE maana In zabar Masa wacce zai aura ,auren wucin gadi, byn Yan watanni sai yarabu d matar.

Abba yace haba ya....ah ah kaga kayi shiru kawai ayimasa AUREN WATA SHIDDA da lokaci yyi yarabu da ita,in Kuma kafison aganka me mgn biyu to.

Shiru Abba yyi Yana tunanin wannan maganar, yyinda uban gayyar bece uffanba saima ya fice dg parlourn....


Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story & written by
 mmn fareesa


Dedicate to all my fans๐Ÿฅฐ๐Ÿฅฐ๐Ÿ‘๐Ÿป❤
ana mugun tare ,naga comments had'e da fatan alkhairi agareni a grps daban daban nagode sosai๐Ÿ™๐Ÿป


p10


"""Ransa bbu dad'i ya isa part nasa" kwanciya yyi Yana tunanin wane irin haline da mom ?"
Tsaki yaja yafi ak'irga , yyinda yakudiri niyar bazai cewa mom komai ba gameda auren datakeso tamasa ,Kuma shima abban bazai Masa mgn ba ,inhar sun tursasa to zai amince amma duk wacce aka aura Masa wlh zata raina kanta agunsa...
Yo inbacin abin mom koni da kaina sai in bud'e campanin da gumina ba sai wani yabudeminba , yafad'a afili had'e da tashi ya wuce bath room...
     Washe gari byn Abdallah yagama Shirin yyi break fast sannan yabar riyanatu na gyara Gurin ya nufi part din iyayansa Dan gaidasu.
Tab'e baki riyanatu tayi  byn ya fita sbd ganin yadda yaketa cika Yana  batsewa,amma ta lura yau Yana cikin damuwa,dan fuskar nan tasa murtuk take tamkar besan miye dariya ba...

apart d'in mom yafara zuwa ya gaida ita ,ta amsa cikin kulawa , sannan ta ce my son kayi hakuri pls kaji wlh zeenat tayi nadamar abinda ta maka Kuma anjima zatazo tabaka hakuri.ina umartarka daka nuna mata ka amince  sbd yarinyar nan tana sonka ai yakamata ka Mata uziri sbd fa Kai take kishi ,shiyasa tayi hakan....amma mom Kuma sbd rashin hankali d wayo had'e da sakarci sai ta zargemu ni wlh banison.....ya isa haka kada kace komai..
Sannan mgnar auren da zaa maka yakake gani?"dan gsky banison wannan campanin yawuce ka....haba mom niwlh banison kina haka ko be budemunba inada kud'i kin sani,Abba  ma  haka zai iya bud'e mun can....ah ah my son wayace maka ana maida hannun kyauta ni na rigada na tsaba  maka wacce zaka aura byn wata shidda ku rabu kaga baza a zargekaba da auri saki. Tunda mahaifinka yyi subutar bakiyace kanada aure be kamata Kuma aji ba haka bane gsky...

Shiru yyi Yana sauraronta " can yace nifa mom banida wani zab'i saidai daza a fasa auren harda na zeenat d'in to zanfi kowa farin ciki wlh...,,,,,


      Hmmmm baza a fasaba kuwa nagaya maka mungama mgn da abbanka ko"

Tashi yyi hade da cewa to mom , yafad'a fuska bbu walwala... murmushi mom tayi tace na zauna nayi tunanin da wa Zan hadaka ?"sai na tuna da mai aikinka RIYANATU.....

Whattttttttt?" Mikike nufi mom?"

Zauna kaji Mana my son inmaka bayani sbd inada hujjojin yin haka zaifi"

Zama yyi had'e da tsareta d ido"ahankali tace kaga dai da farko iyayenta talakawa be Kuma ba nan garin sukeba ada ,amma yaxun sundawo da zama anan inaso kuyi AUREN WATA SHIDDA da ita akuma sirri nafiso dg mu iyayenka sai Kai d ita kawai zaku sani sai zeenat shima sbd kada ta tashi hankalintane.

Munyi mgn da dad naka gobe zai tura alh bukar yaga mamanta suyi mgn akan suna neman aurenta Nanda sati3 zuwa 4 zaayi auren.
     In har sun amince to zasu siya ma ,mamanta gd subata jari ta Kuma saka amata binkice akanka kasan aure' dole Saida binkice in ma tana shakkun bada y'ar tata.
Saidai baaxa a fadi AUREN contract bane zaa dai nuna kana bukatar auren d wuri ita Kuma yarinyar Zan tsorata ta akan dole ta amince in iyayenta suka tambayi tana sonka , sannan Zan Mata alkawarin mai da ita boko sbd harira ta fad'a mun dg JSCE ta tsaya....

Shiru Abdallah yyi yanajin dogon sharhin mom harta Kai aya azancenta"

Tamkar zai fashe sbd bacin rai ,sbd ganin Wai kamarshi zaa tsorata wata can akan tace tana sonsa Wai ta auresa ,Kuma Wai duk arasama  wadda zaa ce a aura Masa sai wannan vileger girl d'in k'aramar yarinya mittsss yaja tsaki afili....


Azabure mom tace nikakewa tsaki abdallah?"

Da sauri yace ah ah mom tunanin zuci nake kiyi hkri pls"

Shiru tayi tana mamakin halinsa, sannan ta ce yanxun kaje gun abbanka ka gaidashi sannan ka koma part naka ka turomun wannan yarinyar....

To"yafad'a atakaice, sannan ya fice dg parlourn.


Koda ya shige part d'in abban,samunsa yyi zai fito ya shirya da alama fita zaiyi,fadawa jikinsa yyi tamkar yaro yasaki kuka.,,,

Da sauri Abba yace yah Salam"

My son gayamun damuwarka kaji ?"

Ahankali yace gsky Abba Ni banson auren nan Dan ALLAH ku barni... ajiyar zuciya Abba yyi hade da cewa to shikenan tunda kafison in kunyata agaban babban mutum irin yallabai yadauki mahaifinka mak'aryaci Abdallah na fasa yimaka auren...bazanso sakaka adamuwaba" saidai matsalar  mominka da k'yar zata....Abba na amince kayi hakuri Dan ALLAH insha ALLAH zankasance mai biyayya agareku.

Murmushi Abba yyi yace yauwa yaron Abba ko kaifa ,ka daure sbd nasan Kai jarimine insha ALLAH inaji ajikina akwai wani babban al'a mari mai kyau ko akasin haka da zai faru nan gaba , sannan wannan auren na sirrine bazayi shagaliba sbd gudun kada agane sai yanzun zakayi aure nafison aganka d matar ranar bikin bud'e campanin insha ALLAH sbd baniso mai girma president yaji lbarin bikin ,inhar sun amince iyayanta zasu baka ita,to da'a d'aura aure washe gari ta tare bbu wata bidia ko al'ada daza ayi.

Sannan apart naka dake gdn nan zaku zauna,ka fahimta?"

ak'agare Abdallah yace eh sbd yadda yakejin zafin maganar auren.... sannan yajanye jikinsa dg na Abba had'e da cewa to Abba sai kadawo, yafad'a had'e da saurin varin Gurin...


Azuciye ya isa part nasa,yasami riyanatu zaune kan carpet tana kallon indiyan firm a receiver"ke kije inji mom.....batamasan ya shigowa b.

Atsawace yace keee eeee!wawiyar inace?" anamiki mgn, atsorace ta juyo sukayi 4 eyes wata uwar harara ya aiko mata da ita had'e da Jan doguwar tsuka,yace kije momna kiranki , sannan kada ki koma yimun kallo a parlou"kinji ko bakijiba?" Yafad'a atsawace....

Jiki na kirma tace naji, had'e da saurin fita t nufi part d'in mom...


Zaune tasami mom itada aminiyar hjy ikilima wato mahaifiyar zeenat, sallama riyanatu tayi gabanta na mugun faduwa sbd tana mugun jin tsoron mom had'e da shakkarta.

Sama d qasa suka kalleta hjy ikilima ta tabe baki .sannan mom taja tsaki hade da hararan riyanatu dake gaidasu tace ki rik'e gaisuwarki.

Tuni mom ta Fara mgn kamar haka ,dalilin kiranki shine inason saki wani aiki mai hadari saidai zanmki GARGADI 2 na farko kiyi shiru kada ki fadawa kowa na biyu dole ki amince ko kuwa duniyar ta gagareki Zama....zaro ido riyanatu tayi cikinta yyi k'ara k'uuuuuuuuuuu tuni xufa tafara keto Mata.... murmushn samun nassara mom tayi sannan ta zayyane wa riyanatu k'udirinta akan son ta auri Abdallah Kuma AUREN WATA SHIDDA....

Cikin tsoro riyanatu tace Dan ALLAH hjy kirufamun asiri wlh tsoronsa nake ......rufemin baki ai na Masa mgn bbu abinda zai Miki sbd shi mgn Bata sha Masa kaiba saiki kiyaye kada kimasa kuskure akwai dalili shiyasa Zaki auresa inba hakaba ai ke ko darajar matar direbansa Baki kaiba.

daga k'arshe gobe zaa je gdnku gun ummanki neman aurenki inta amince ta fad'a musu suje gun iyayanki maza abasu aurenki.

Sannan inaso ki nunama ummnki kinason Abdallah Kuma soyayya kuke dashi....

Cikin tsoro riyanatu tace Amma Dan ALLAH kada kimun komai sannan da way shidda yyi zai sakeni?"

Harararta mom tayi tace eh bbu ragi bbu k'ari ,saiki tafi ko!kin wani kama kallonku d k'wala kwalan idanunki....


Jiki asanyaye Riyanatu ta fice ta na mamakin meke Shirin faruwa d rayuwarsu itada  ummanta be?"

Tasan in bata amsaba to komai mom zata iya yimata sbd tunda taji maganarsu rannan ta yarda hjy batada Imani.

Da haka ta koma part d'in Abdallah,tasamu bayan nan,haka ta zauna tana tunani har 12 tayi,saiga wani yyi knock ta bud'e nan yasanar da ita shine zai rik'a koya Mata turanci .
     Babu musu ta bisa alambun gdn yafara koyar da ita.
Cikin ikon ALLAH kafin su tashi riyanatu ta iya wasu abubuwa,shi kansa malamin  yyi mamakin k'wak'walwarta....

Byn sun tashi dg islamiya ta koma gd ,duk jikinta asanyaye Fatima na lura da ita,harta tambayeta Amma sai tace bbu koma.


***********
Washe gari Gurin karfe 2:30pm su umma na zaune atsakar gd suna fira yyinda mutane na zuwa siyan abinci...wani yaro yashigo yace Wai ance ana son mgn da umman riyanatu inji wani mutum....

Da mamaki zuwaira tace to kace tana zuwa.

Byn fitar yaron ,umma tacewa mama zuwaira tayi hkri ita bazata b sbd batasan kowa agarinba.

Murmushi zuwaira tayi sannan ta saaka hijab ta fice waje.....tafi minti12 sannan ta dawo tana murmushi ta kalli umma tace kisaka hijab naki muje soro bara na shimfad'a ta barma bak'i mukayi sunxo mgn da kene akan dansu nason riyanatu....


Umma tace....


Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



   Story & written by
    mmn fareesa


Wannan shafin nakune
Queen
Fatimatou
Mmn Bilkisu
Sury baby
Bilkisu Auwal
Zee hamis wada
Queen mimi
Inajindadin comments naku sosai love u wujiga wujiga๐Ÿ‘๐Ÿป๐Ÿฅฐ๐Ÿฅฐ


p11


Umma tace anya kuwa da gaskene?"
Murmushi zuwaira tayi tace muje Dan ALLAH!ta fad'a had'e da daukar tabarma ta nufi soro....
Umma ma tasaka hijab tabi bayanta ranta fal da tunani"
       sallama tayi had'e da Zama kusada zuwaira" byn gama gaisawa,alh bukar yyi gyaran murya had'e da cewa to nasandai zakuyi mamakin ganina a wannan lokaci,suna Alh Abubakar da'aki sani da alh buka .nasan kunsan ALH KABIR GIRMA ko?"suka d'aga Kai" sannan yacigaba da cewa ni amininsane  yaturoni akan neman iziniku akan zaya turo a nema ma D'ansa auren y'ar ku,wato RIYANATU dake ma D'ansa aiki,wato ABDALLAH dg nan suka Fara soyayya d juna ....
     Cikin mamaki umma tace  oh D'an yau kenan dama  ba aiki takemasa ba soyayya suke?"
Murmushi alh bukar yyi hade da cewa kunsan halin Yara insunason Abu to shine ai Abdallah ya matsa ayimusu aure saita cigaba da karatunta acan insha ALLAH,amma yanxun miye amsar ku?" Umma tayi ajiyar zuciya had'e da cewa da farko dai sai naji ta bakinta intana sonsa sannan muyi binkice akansa d iyayensa tukum saina turaku gun dangin mahaifinta dake k'auyen...


     Tashi alh bukar yyi hade da yimusu godiya sannan ya ajiye musu rafa guda ta 1K ya fice Yana cewa ah ah su karb'a sbd jin umma na cewa yabar kud'insa...
byn fitar sa,su umma suka shiga cikin gd"mama zuwaira nata murmushi tace oh ikon ALLAH Ashe alkhairi ne ya maidoku garin nan,ai dama matar mutum kabarinsa ALLAH yasa hakan shiyafi alkhairi.
Umma tace ameen, Amma nifa gsky inajin tsoron ta auresa mufa talakawane gara dai ta auri talaka daidai mu. Kuma bamusan halinsaba....ah ah bintu addua yaka Mata kiyi, maganar hali Kuma gsky dukda ba Wai hudda nikedasu ba to Alh Kabir girma Yana mutunci sosai akwai temakon talakawa wlh ga yadda naji ,Kuma shi Abdallah bama nan yyi karatu ba ,bedade d dawowaba ,Amma inbaki yardaba bara nasaka harira dake hudd'a su dakuma salisu mak'ocinmu dake dreban gdn su Miki binkice akansu..
Ajiyar zuciya umma tayi tace ai bama wannan ba ,sai tazo naji abakinta tukum kinsan Dan yau ,kahaifesa baka haifi halinsaba.
Zuwaira tace hakane tana dariya , yyinda Fatima dake sauraronsu tanad'aki taita murmushi tana tuna yau zata tsokani Riyanatu....

    *********
Zaune yake a lambun gdn kan resting cheir. gabansa center table ne da choke d cup akai da riyanatu ta aje Masa"
Idonsa alumshe yaje sai girgiza Kai yake,Yana jiran zuwan  Hafiz sbd yakirasa akan yazo yanxun yanason ganinsa...
Yyi zurfi atunani yaji andafa kafad'arsa "da sauri yabude idanunsa dake jajir ya aza akan fuskar Hafiz"tamkar bayason mgn yace pls kazauna friend"
    zama Hafiz yyi had'e da cewa lfy dai ko AK?"
cikin damuwa yasanar da shi maganar AUREN WATA SHIDDA da mom ke son tamasa Kuma Wai wannan vileger girl d'in ta zab'a Masa.....hhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhh...look mlm ba dariya nakiraka kamunba ,shawara zaka bani pls"cewar AK cikin jin haushin Hafiz daketa Masa dariyar.kallonsa Hafiz yyi ido cikin ido yace gsky kaji dad'i wlh... mittsss kaifa d'aniska ne ,Ina maka wani zance Kai kanamun wani"murmushi Hafiz yyi had'e da cewa hmmm to Wai miye abin damuwa anan ai gara RIYANATU akan zeenat gsky Ina maka murna sbd yarinyar ta had'u wlh ๐Ÿ’ฏ% inbacin daka rigani aida nike Shirin yin ta biyu da ita ni wlh dama tuni naga kunyi mugun marching da ita harfa kama na ga kunayi  da ita,sbd.....STOP IT kanada  matsala wlh kaxo kanamun surutan banza, bacin bashi na kiraka kamunba...wlh zaka jamata wlh ....
     Sorry abokina Ni gsky banison kayi auren contract,amma kayi biyayya gasu Abba amma insha ALLAH wannan auren zai Zama alkhairi ,Kuma insha ALLAH baza ka auri zeenat ba.
Tsaki abdallah yaja had'e da cewa suduka bbu choice dina aciki kinsu .....hmmm haba mutumin kadafa ka kamu kazo kana mun y'ar murya nashawo maka kanta , Hafiz yafad'a cikin tsokana....wani purch Abdallah yakawo Masa yyi saurin kaucewa Yana dariya had'e da cewa k'ila mu angwance tare k'ila ma na rigaka sbd ni gsky bbu d,aga k'afa in my feedo ta shigo hannu na yadda nike amatse....tsaki abdallah yaja had'e da cewa banxa Dan akuya... murmushi Hafiz yyi had'e da cewa eh naji kaikuma  me zaa kiraka sbd gara ni da Kai....kayimun shiru ga wannan yarinyar nan karma kaja ta kamun raini wlh na fasa bakinta yafad'a in a serious tone...

Riyanatu na k'arasowa,ta sunkuyar dakanta k'asa sannan tace yallabai ko akwai aikin da zanyi maka lokacin islamiya yakusa?"

inkin tanka Abdallah yatanka saima yarufe ido had'e jingina jikin sa d kujerar yamata banza.,,,

dagowa tayi ganin yashareta tace Yaya hafis Ina wuni?"

Murmushi Hafiz yyi yace lfy qlau ,Ashe kina islamiya?"

Eh tafad'a"atakaice.

Kallon AK hafis yyi hade da cewa friend kayi mgn pls kabarta tsaye "kada Kuma ta tafi tayi laifi..

Yakusan second 52 , sannan ya tsina fuska cikin husky voice ya dubeta had'e makamata harara sannan yace ban hanaki kirana da yallabai ba saikace kina gaban d'an sanda mittsss,Wai miyasa inbaki sani surutuba,bakijin dad'i?"

"Ahankali tace kayi hakuri lokaci na tafiya me zanyi?"

Banza yyi da ita"

Hafiy dake kallon su yace riyanatu kitafi abinki kinji...


Juyawa tayi had'e da tafiya.....RIYANNNNNNN cak ta tsaya sbd jin muryar Abdallah ta daki dodon kunnanta , had'e da mamakin jin yafad'i sunanta dukda yarage wasu haruffan aciki,Kuma yau ce ranar daya Fara Kiran sunanta.,sai Kuma taji sunan yyi mugun Mata dad'i amma Bata nuna ba.

Ahankali tace tadawo baya had'e da cewa gani,yadauki wasu second kafin yace ki had'a mun ruwan wanka,saiki tafi....

"To tace had'e da tafiya"

Byn tafiyita Hafiz yabugi kafad'ar Abdallah yace gsky mutumin kana lokaci fa wannan kasaita haka ,kumafa sunan da ka kirata dashi yyi daidai dama haka ake kiranta wlh RIYAN nice name.... Ya isa parrot Kanata zuba kamar ruwa na kirata ne sbd bazan iya kiran sunan har k'arsheba sbd yyimun tsawo sunan...

Murmushi Hafiz yyi had'e da girgiza Kai suka cigaba d fira wacce afirar Hafiz ne yafi mgn.,,,,,,


Riyanatu ce zaune gaban umma "

Umma tace dama Ashe ba aiki kikeba soyayya kuke da yaron nan dama?"

Wani mugun faduwa gaban riyanatu yyi ,cikin dauriya ta kak'aro murmushi ta sunkuyar dakanta k'asa..

Tunani take wato Ashe harma anzo neman auren kenan?"tunda gashi har umma na Mata maganar, lallai hjy abin tsoroce ita yanxun to yanxun daukar suna soyayya da Abdallah ake Mata wannan mai girman kan tsiyar d izza...kin yi shiru bakiyi mgn ba, iyayensa sun Aiko suna son abasu damar suje su nema Masa aurenki.

Kifad'amun  gsky kina sonsa ko kuwa?" Cewar umma tana kallon riyanatu...

Shiru tayi tana mamaki  da wannan tsaka mai wuya datake aciki"

Umma tace kinyi shiru ,kada kiji kunya kinji kifad'amun abinda ke ranki...

Ahankali tace...


Share pls

BY 
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story & written by
     mmn fareesa


Masumin mgn a pc ko agrps bbu reply kuyi hakuri pls &pls dakuma rashin jin posting d'ina inada uzuri....


p12

    "Ahankali tace eh umma"ta fad'a tana murmushn dole had'e rufe fuskarta Wai taji kunya....
dariya umma tayi hade da cewa ALLAH yatabbatar Mana d alkhairi.sannan cike da jin kunya riyanatu ta tashi t fice..
    Aranan ba'a kwanaba umma ta Kira Inna mariya tasanar da ita had'e da neman shawarar ta" takuma amince cikin farin ciki had'e da musu fatan alkhairi bbu bata lokaci umma ta bukaci Inna mariya ta sanar da baffa sule(k'anin baban riyanatu)zuwan bak'in yakuma fad'i yaushe zasu zo?"
sannan sukayi sallama akan duk yadda sukayi zata saka gali yakira su umma tamasu baya ni...

      Zaune yake a cikin mota dawowarsa kenan dg wani park,kasancewar da kansa yyi driving bbu Wanda yabisa, ya d'ora kansa bisa sitiyarin na motor yyi zurfi atunani.... k'amshin turarenta da motsin bud'e motar datayi yasakashi dawowa tunaninsa"hiiii baby!
d'agowa yyi ransa bbu dad'i fuska a had'e yadubeta ya juya Kai , azuciyarsa yyi tsaki sbd ganin irin kayan dake jikinta... ahankali tace yakk?
lfy!ya amsa atakaice"haba baby duk kawani daure fuska bbu faraa kasan banason haka ko?"look zeet kinsan halina banason surutu da yawan mgn so pls ya isa"murmushi tayi tace hakane baby amma yakamata kaji meke tafe dani,kasan inasonka sosai am ma Kai ko irin zuwa fira guna bakason yi miyasa ?"cikin k'osawa yace hakan baya cikin tsarina"
Yanzun gsky yakamata kaje gdnmu ayi mgn asan da Kai dna kammala skul muyi AURE....ki sanar da su Mana ni ....haba Mana baby?"Kinga ki barni inji da damuwata mom ma AUREN WATA SHIDDA zatamun da time yacika narabu d matar na aureki shikenan?"yafad'a Yana kallonta da sexy eyes nasa.
   Tasoyi Masa bore amma sbd yadda yatsaare ta ido dakuma cewar zai aureta sai tayi lak'os dukda dama tasan da maganar aurensa sbd mominta ta gayamata ,amma bataso riyanatu ce ba wadda za'ayi auren d ita" sbd batasan miyasa data ganta takejin faduwar gaba ba?"
sannan kyawun yarinyar na Bata tsoro.
cikin kissa tace amma dai bbu abinda zai shiga tsakanunku d ita in...keeeeeeeeee! mikike nufi?" banason hauka fa yafad'a atsawace.... murmushi tayi had'e da cewa yauwa baby  har naji Dadi dakake nuna kinta... murmushn takaici yyi hade da cewa my zeenat Kenan ai Kisha kuruminki ke ce zabina...wani ihun murna tayi had'e da kokarin hugging nasa...kallon daya Aiko Mata dashi yasata dakatawa sbd yadda yyi mugun tsare gd,tsaki yaja had'e da ficewa dg motar yabarta ciki,Yana mamakin rashin wayonta tana classic lady amma harta yarda itace zabinnsa....


Part nasa ya wuce , parlour yasami riyanatu na turere parlourn,iya lab'b'ansa yyi sallama ,ita kuwa azatonta bayama sallama sbd girman kan sa,batasan budeymurya yyine ke be iyawa.
Ko kallensa batayiba tacigaba da aikinta.
Zama yyi kan kujera ya aza k'afa daya kan daya Yana wani Shan k'amshi"can yadubeta ak'ule hade da cewa keeeeeee! wace irin sokuwa ce Wai?" bakisan mutum yadawo kimasa sannu ko ki kamasa  ruwa balle Kuma ki kaiga tambayar sa yana buk'atar wani Abu ke kin Fara wayewa ko?"
    Shiru tayi had'e da mugun mamakinsa ,shin Wai shi wane irin mutum ne? in an kulasa yyimaka banza Inka k'yalesa shima laifine kenan"ko bakya jine?"
da sauri tace ah ah kayi hakuri naji bakayi...in ...um sal....what!mikikeson cewa?" Oh nagane kina nufin banyi sallama ba ko?" wato ni Zaki gayawa mgn ko kinunamun bansan darajan addininaba ko meye?" da sauri tace nifa ba haka nake nufi ba....dallah yimun shiru Kona fasa Miki Baki stupid kawai kinzo kina sani surutu mittsss yaja tsaki hade da cewa dallah kamun ruwa..."ahankali tace ALLAH yahuci xuciyarka"
Byn ta kawo ruwan ta zuba Masa had'e da mik'a Masa,tana tsugunne yashanye sannan ta d'auke cup d robar ,Bata kallesa tace zakayi wanka ne?"
Saida yadauki wasu mintina tukum sannan yace keeeee zonan!jikinta na rawa ta juyo had'e da kallonsa tace kayi hakuri intambayar ta maka zafi...Wai ba cewa nayi kizoba " cikin tsoro ta duk'a kusada k'afafunsa yyinda yyimata mugun kwarjini ta kasa kallonsa.


Cikin isa yace nasan mom tasanar dake aurenki dazata kikamun ko?"

To inaso  kisani bawai son AUREN WATA SHIDDAn nikeba Zan Mata biyayya nekawai sbd haka ko byn anyi auren zanrabu dake ,shawara d'aya zanbaki shine kada ki yarda zuciyarki ta SONI sbd ni bazan taba SONKI ba "

Shiru tayi tana mamakin Wai mi mutumin nan yadauki kansane ?"itafa gsky  tagaji da wannan wulakancin nasa, sai kace kud'i haukane"shibaisan wannan abun dayake Mata ba mugun tsanarsa takeji,cikin dakiya tace hmmm BOTH kenan ai inkmayi tunanin ni riyanatu zansoka kayi kuskure sbd bazan tab'a son mutum irinkaba wlh"....zaro ido yyi sbd mugun mamaki da maganarta tabashi Amma be nuna mamakinba cikin daurewar fuska yace ke ni Zaki gayama mgn sbd kin samu guri ko?" to bari kiji zanyi pernishment naki"ahankali tace pls sorry both nafad'a maka gasky tane... shout up!ok no zki nunawa ma kin waye kin Fara jin English ko to as from today kada ki koma kirana da both inba Zaki iya cewa Abdallah ba ki bari "stupid girl kawai "inkin gadama ki had'a mun ruwan wanka and last ki fitomin da k'ananun kaya  sbd gulma shine d'azun da safe kika fitomin da manyan kaya ko sbd kin rainani....amma ai sune al'adarka ko?"
bansaniba Ina ruwanki to ma!naje nak'i Al adar"
girgiza Kai tayi had'e da nufar  bed room nasa tabarsa aparlou.


Batafi 6 minit ba ta dawo....turus tayi had'e da jin faduwar gaba sbd 4 eyes dasukayi da mom"
jiki n rawa ta duk'a had'e da cewa hjy Ina wuni?"

Lfy" mom ta amsa atakaice tana Yan Harare Harare...

Cikin isa had'e da bada order tace ke yau bazaki islamiya ba ,kitsaya ki kularmun da yaro anguwa zanje, tafad'a had'e da gallawa riyanatu harara"jikinta na kirma tace to hjy.

Tsaki mom tayi ta dubi Abdallah had'e da cewa sai nadawo my son ka kularmun da kanka kaji"

Murmushi yyi yace insha ALLAH mom, ALLAH yatsare.

"Tace Amin had'e da ficewa"

Riyanatu dake zaune  cike da jin haushinsu dg shi har mom d'in sbd hanata zuwa islamiya da akayi ,tunani take wai akan wannan k'aton saikace wani yaro ace ta wani kula dashi ,shiko kunya bayaji ace komai sai an Masa toda basuda kudinfa?"

K'arar rufe kofar bed room d'in yasa ta gane yabar parlourn" tsaki taja afili tace ALLAH ka kamun k'arshen matsalar nan....

Byn minti 15 tashiga ciki sbd ta fito Masa da kayansa.

Koda ta duba wardrobe nasa,k'ananun kaya ta fito Masa da su ,jeans dark blue da red d'in t shirt ta aje gefen gado, sannan ta fice jin Yana kokarin fitowa.

Komawa tayi a parlou ta zauna ta Fara kuka sbd bacin rai da tunanin wannan aure da zaa lakaba Mata watanni kad'an amai da ita k'aramar zawara...zaro ido tayi sbd wani tunani datayi,afili tace yah Salam insha ALLAH bbu abinda zai ahiga taakanunmu "to Wai ni miyasa ma na amince wai?"

Share hawanta tayi sbd jin zai bud'e parlourn.

Wani fitinan nan kamshi ketashi ajikinsa ,Saida ta lumshe ido"ko inda take be kallaba ya hakimce kan kujera.

Koda ta ga haka dining area ta nufa ta kwaso mai takawo gabansa tayi serving nasa, had'e da cewa kaci abinci pls"

Murmushi ya kuce Masa sbd ganin tana wani yin mgn cikin rarrashi wato taji maganar mom kenan.

Bbu musu yadan ci bbu laifi ,ta zuba Masa ruwa d drink yasha...

Byn  ya idar ,yajawo laptop Yana dubawa can Kuma taga yashige bed room Jim kad'an yafito da pen d katuwar paper yafara Zane cikin kwarewa....sai satar kallon sa take "cikin 30 minit ya ajiye yafice zuwa masjid sallar la'asar.

Tashi tayi cikin sand'a ta duba zanen datayi,zaro ido tayi sbd ganin yadda ya Zane mutum sak tamkar hoto da alama photo ne ya kalla yyi zanen"

Ajiye tayi tana mamakin kwarewarsa azane"

Sannan taje tayi Sallah itama"

Sadda ta dawo har yadawo yadan kwanta kan 3 seeter"yatsina fuska yyi hade da cewa keeeeeee zanyi bacci bansan yawan motsi sbd dakinyi sai naji.

Cikin mamakin isarsa tace kana nufin da Raina bazanyi motsiba?"

"bansaniba"

Yafad'a had'e da gyara kwanciyarsa yarufe ido.

Sunkai kusan 35 minit , sannan cikin sand'a ta tashi ahankali zata fice..keeeeeeee! yafad'a cikin husky voice d'in sa,jikinta na kirma ta tsaya cak sbd batasan Yana kallonta ta k'asan ido"

Azuciyarta tace oh ni nabani d Mr arrogant din nร n....zonan nace" muryarsa ta katse Mata tunani.

Gabanta na faduwa ta je nesa dashi had'e da cewa gani!

Dagowa yyi ya bankomata harara sannan yace dama kula da ni mom tace kiyi ko kuwa sakani surutu kisamin ciwon Kai?

Girgiza Kai tayi had'e da cewa kayi h...short up your mouth stupit bacemun da gani...sum sum ta wuce ta Sami guri ta zauna.

Kwanciya yyi hade komawa bacci"

Be farkaba sai 6:21pm da sauri ya wuce ciki yyi alwarlal magrib yafito yadubeta cikin yatsina fuska yace Zaki iya tafiya gd" bejira amsarta ba yafice.

Tabe baki tayi had'e da gyara hijab nata ta dauki Jakarta ,ta fito parking space tasamu ya'u direba na alwalla (shike mai da ita gd kullum) yace ta jira yyi Sallah.


Byn ya ya'u direba yadawo yasameta inda yabarta wato bakin get , sannan suka wuce gd.

Bayan kwana2...

Share pls


BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
    Mmn fareesa


p13

   *Bayan kwana2*

Abubuwa sun faru inda Inna mariya ta sanar da baffa sule k'anin baban riyanatu zuwan bak'in yakuma yi murna sosai sbd jin wannan magana, yasan insha ALLAH barinsu garinsu alkhairi ne"
hakan yasa yacewa mariya duk ranar dazasu zo suxo yyi .
      bbu musu inna mariya tasanar da umma komai,ita Kuma ta sanar da Alh bukar sbd yazo ranar da umma sukayi waya d Inna mariya har take sanar Mata gali na cikin damuwa sbd jin labarin auren riyanatu Wai sonta  yake Amma be fad'a ba tuni."
Cikin jin tausayinsa umma tace oh ikon ALLAH !gsky banji dad'i ba , ALLAH yabasa wacce ta fita, k'ila ita ba alkhairi bace agunsa.. inna mariya tace Amin sukayi sallama.,,,

    "Gefe guda Kuma riyanatu bbu laifi tana gane turancin sosai ,sbd hakan teachern nata yake had'a Mata da wasu abubuwan"
Sannan yasanar da Abdallah tunda wannan week d'in za'a koma skul kawai yasaka ta zaifi"shikuwa yace saiya duba.
Yyinda ita Fatima nakokarin ganin riyanatu ta xama classic lady itama,hakan yasa ana Bata albashinta sukaje bortique ta zabo Mata k'ananun kaya masu saukin siya "bakuma masu fidar da tsiraiciba"
    Had'e da kayan kwaliya tuni riyanatu ta shiga sahu itama lolx..๐Ÿคฃ

    ***********
Yau yakama Sunday akuma yau da marece Fatima zata koma skul"
Tun safe riyanatu tayi shirinta bbu k'arya,dukda ba tasoba sbd gudun Abdallah ya yarfata to Amma  tilas Fatima ta Mata sbd ita azaton Fatima kwalliyar zata burge Abdallah hakan yasa da ita sukayi kwalliyar,hmmm duk Wanda yasanta inba farin sani ka mataba to bazaka ganeta.
Sanye take da gownt maroon da veil bak'i tayi rolling, ga  takalmi bak'i flat tasaka da Yar hand bag , yyinda lips d'in ta sukasha  lip stick maroon "sannan Fatima ta fesheta da body sprays.
      Fuska bbu walwala ta fito dg daki sbd tafiyar Fatima skul tasan Kuma sadda zata dawo dg gun aiki ta koma skul ga wannane kwalliyar,,ita tsoronta ma kada mom ta gani ta Mata wani zato....kin fito ne ,cewar umma dake tasbihi azuciyarta sbd ganin yadda  yar tata tayi kyau.
"Ahankali tace eh umma bara na wuce "umma tace ALLAH yatsare"amma gsky in an tsaida mgn ,to zakibar aikin sbd be daceba , amatsayinki na hausa Fulani ,kikasance me kunya da Kuma tsare mutuncinki .
   Insha ALLAH umma nima nafison na Dena ,ta fad'a had'e da ficewa dg gdn....

"Kamar yadda ta Saba haka ta gyare ko Ina "sannan ta had'a Masa ruwan wanka kafin ta fito a parlou tayi jiran fitowarsa .
Shiru tayi tana tunanin kada Abdallah yyi zaton sbd taja hankalinsa tayi kwalli haka !Kai kodai ta gogene...salamu alaikum, sallamar Hafiz ta katse Mata tunani... murmushi tayi had'e da amsawa suka gaisa, sannan tace oh Yaya hafis kwana2 nabar ganinka"y'ar dariya yyi yace wlh RIYAN kinsan bikina yakusa befi 10 days ba shiyasa naje Kuma kano sbd ammi na anmata transfer a hospital tadawo anan garin da aiki ,jiya muka sauka,shine nazo gun ogan naki nakawo gaisuwa sbd jiya naga 2miss call nasa,nakira be d'agaba nasan fushi yyi.tabe Baki riyanatu tayi had'e da cewa to ALLAH yasa alkhairi"
Yyi saurin cewa amin,Zama yyi Yana murmushi sbd ganin kyawun datayi har cikin ransa yanama abokinsa fatan mallakarta har abada."
Ahankali tace to a Ina amaryar tamu takene?"murmushi yyi yace y'ar nan garince ai,Kuma nan zamu zauna duk fg Ni har ammina aiki yakamu nan garin. "ajiyar zuciya tayi had'e da cewa to ai yanxun ka Zama Dan gari ai.
Kofar bed room d'in yakalla sannan yace hakane,amma zakije  bikina ko ,ma'ana kiyi attending d'in duk event na bikin?"
    Kafin tayi mgn Abdallah ya murd'a kofar yashigo parlourn...tuni k'amshinsa ya mamaye parlourn"fuska murtuk ya gallawa hafis harara had'e da cewa parrot kazo ka cikawa mutane parlour da mgn " yafad'a had'e da Zama gefen hafis dake dariya"
Ahankali tace barka da fitowa!
dagowa yyi sukayi 4eyes...k'uri yyimata sbd son gano shin itace ko ba ita bace sbd yadda tayi kyau na ban mamaki...yanxun zakayi break ne?"muryarta ta katse masa  tunani,saurin barin kalleta yyi cike d basarwa ,yawani yamutsa fuska tamkar yaga abin k'ii yace eh akan labb'ansa...
Hafis da tunda yaga Abdallah yad'ago zai kalleta yakafesa d ido... murmushi kawai yake mai sauti,"ahankali yace AK dakai fa take yakamata kadawo hayyacinka... mittsss Abdallah ya ja doguwar tsuka had'e da cewa dallah mlm miye haka?"kamar ya nadawo hayyavina ,daba a hayyacina nakeba ko me??""
nidai bance hakaba maida wukar...cewar Hafiz Yana dariya.
Yyinda riyanatu ke saurarensu Amma Bata kallonsu.


Keeeee! Kije ki kamun break kinyiwa mutane wani zaune sai kace kina gaban sa'anninki.. mitttsss yaja tsaki hade da makawa Hafiz harara ganin zaiyi mgn.

Ahankali ta tashi ta fice"

Hafiz yace haba mutumin kana yadda kakeso wlh wannan iko haka ai kabari abiya sadakin ko, sannan da alama wannan kwalliyar tata ,tatafi d imaninka....stop it !inkasan wannan surutun yakawoka guna zaka iya tafiya "wato namalura sokake da gske na auri wannan yarinyar ko?"

Hmmm friend kenan abar maganar kawai,dama naga Miss call naka jiya ,nakira kak'i dagawa sorry kasan jiya muka dawo tare d ammi bana kusa da wayar , sannan my feedo ta dameni da rigima tanason kuje kuga k'awayenta abasu abinda zaa basu ,kasan in tanamun wannan rigimar wlh jinake tamkar nacika aiki kaima ka gane?"yafad'a Yana daga gira had'e da murmushi,tsaki abdallah yaja had'e da cewa aikin banza jarababbe ai garadai da ammi zata maka aure wlh, sannan batun ganin k'awayenta zamu iya zuwa Amma kasan banason surutu da hayaniya Mata 2 sun isa muyi mgn da su.... murmushi Hafiz yyi had'e da cewa relax Mana ai nafad'a musu anbadakai๐Ÿ˜‚ dud da nasan abokin nawa da farin jini dole wata ta k'yasa, shiyasa nafison kuje da babynka RIYAN kawai "itama nafad'a Mata tare zuje takuma amince....


Iya k'uluwa Abdallah ya k'ulu da iskancin da Hafiz ke Masa"murmushn takaici yyi Yana kokarin mgn... riyanatu tayi sallama had'e da ajiye musu tray din a gabansu "

Kok'arin had'ama Abdallah tea takeyi ,yyi saurin dakatar da ita ,cikin mugun tsare gd yace ke wakikayiwa kwalliya?"

Mamaki sosae tayi da tambayar sa, azuciyarta tace zanyi maganinka kuwa....

"Ko bakya jine?"

da sauri tace saurayina nayiwa!Wanda in  Zan aura in mun rabu!

atsawace yace keee nikike gayawa saurayinki?"hhhhhhh yyi dariyar rainin hankalin sannan yadubeta off & down yace ai Ni banga wani Abu ajikinki da wani zai gani har ya burgesaba and last nakoma Miki mgn ko tambaya kina bani amsa agadarance Zan nunamiki ainahin calour d'ina....

 Bata ce komai ba "tea din ta mik'a Masa hade plate datayi serving nasa , sannan ta fice dg parlourn Dan tajira awaje su gama.

Hafiz ya girgiza Kai beyi mgn ba,saidai yasha alwashin duk ranar da Abdallah yakamu dason riyanatu bazai taimakesa akan yashawo kantaba Kuma zai gayamasa managar dayake so son ransa...

#######
Abdallah sunje da sauran friends nasu sunga k'awayen fiddausi(feedo)sun basu abinda suka bukata ,acewar Abdallah ai in suntaya akan abinda suka bukata sunyi k'aranta ,da kud'insa yabasu.
     Yyinda duk yawancin Yan matan sun rude da ganin Abdallah duk da sun lura yanada Shan k'amshi had'e da izzah"


Shire Shire kawai ake duka b'angaren 2 Dana Abdallah Dana Hafiz, yyinda Abdallah iyayensa sun je kauye antsaida mgn akan Nanda sati3 za'ayi bikin, sannan riyanatu umma tace ta Dena aiki yau kwanta 3 rabon ta da gdn,mom ta tura harira taji ko lfy"
Sai umma tace lfy lau ta Dena ne in ALLAH yasa tazama matarsa ta Masa komai..
Tabe baki mom tayi dataji bayanin umma gun harira, azuciyarta tace hmmm danbakisan auren yarjejeniya bane shiyasa....

Ayau yakama laraba   Kuma yau ake arebiant night nasu hafis,ga Abdallah ne babban abokin ango , sannan Hafiz yace inhar bada RIYAN zashiba to baya bukatar sa ,da farko yyi fushi yace eh bazashiba tunda Saida ita.
amma dayayi tunanin yadda yakeda Hafiz saiyaji bazai iyaba gashi besan gdnsu RIYAN ba.

Wata arebiant gown ce me masifar kyau da tsada yasiya yakira  ya'u direba, kasancewar yasan gdn sbd ganin Yana maida ita gd.

Yabasa yace yabata ,Kuma yasanar da ita anjima Gurin 5:00 pm zaizo ta shirya tasaka wannan rigai...,,,



Zaune take tana tunanin wannan k'addararran aure da za'amata" umma ta shigo dakin had'e da kallon ta tace kije soro kinada bak'o Abdallah ya aikosa.....

"Wani mugun faduwa gaban ta yyi sbd jin ankira Abdallah"

Cike da mamakin Wai ya aiko wani ta fice zuwa soro.

byn sun gaisa da ya'u direba ,ya mik'o Mata ledar had'e da sanar da ita abinda Abdallah yace....

Cikin k'arfin hali tace to shikenan, sannan sukayi sallama.

Tunani take to Ina zasu insun saka kayan be?" Itafa gsky tanajin tsoro k...har bakon yatafi?" cewar umma dake dubanta.

Murmushi ta k'akaro had'e da cewa eh wlh Wai kayane ya aiko zaizo da karfe5 nasaka zamuje anguwa...

Umma tace to ALLAH yakawosa lfy kidai kula da kanki dukda ansa muku Rana ni banson yawan nan bbu aure atsakani...

    da misalin karfe 4:30 riyanatu ta gama Shirin ta ,sbd gudun masifar Abdallah kada yazo bata shiryaba.
Masha ALLAH tayi masifar kyau tamkar balarabiyar abinka da bafulatana."
   Sai kamshi ketashi ajikinta,byn ta gama shiryawa ta zauna jiran zuwan sa...

Batafi minti12 ba da Zama yaro yashigo da sallama Wai wasu masu motoci sunce RIYAN tazo...

Tana dg cikin daki ta juyo...umma ta k'walo Mata Kira had'e da cewa ta fito.

mama zuwaira ta dubeta tace Masha ALLAH y'ata kinyi kyau"toshi sirikin namu bazai shigo yagaidamuba"

Cikin kak'aro murmushi tace uhmmm mama kunyafa yakeji"umma tace Ni kaina bana ma son yazo wlh... murmushi mama zuwaira ta yi tace oh bintu kunyarku ta Fulani na nan ajininki.

Kallon su riyanatu tayi had'e da cewa bara naje naji ina zamuje ne Wai.

To sukace sannan ta fice......


Yawan comments yawan typing ๐Ÿ˜Ž๐Ÿ˜Ž


Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story & written by
   mmn fareesa


Congratulations mmn sultan Ina taya ki murnar kamla littafinki(SON ZUCIYA)ga Kuma wani sabon salon kin fito da shi a Y'AR SADAKA... ALLAH yasa kifara asaa...


Not edited

p14

   Abdallah zaune acikin mota gdn baya Yana hangen gdnsu RIYAN konace gdn mama zuwaira mai abinci.
Kallon gdn yake cikeda tausayi, azuciyarsa yace oh gsky yarinyar nan basudashi ,Amma ace kamarni ace surukaina na wannan gdn miye anfanin samuna?" Dukda auren wucin gadi zamuyi da time yacika narabu d ita"
     Amma zanga Ibrahim (amintaccen yaronsa) yasiya musu gd su koma.....hango RIYAN da yyi cikin arebiant gown tamkar balarabiyar ko shuwa Arab..lolx.. yakatse Masa tunanin sa.... had'e rai yyi tamkar besan miye dariya ba,ganin cikin guards nasa wani zai bud'e Mata motar"
Sallama tayi , jikinta na b'ari cike da shakkarsa sbd ganin yadda ya had'e rai ,ta tsaya Bata shiga ba"tace ina wuni?"lfy"ya amsa atakaice"sunkai kusan 2 minit tukum yace inbaki shirya tafiyarba zaki iya komawa gd kin wani yimun tsaye akai..."ahankali tace kayi hakuri na shirya ,amma dan ALLAH Ina zamuje ne?"inaso in sanar da umma tukum.
      Harararta yyi yace bansaniba?"mekika d'aukeni be Wai?"ok Zan saidake neko"
Fuska bbu walwala itama tace hmm Ni bahaka nake nufiba !inason sanine dannafad'a agd"be kalleta ba ,yawani yamutsa fuska sannan yace gun event din Hafiz sannan ki sanar da ita cikin 2 minit inkika .wuce haka zamu tafi.,,,

"batace komaiba ta juya zuwa gd"

Batakai 2 minit dinba ta fito ta nufi motar gabanta na faduwa.

Bismillah tayi had'e da shigewa ta takure gu d'aya, sannan ta saci kallonsa sanye yake da jallabiya bak'a me gajeren hannu"bbu hula akansa dayasha gyara sai salk'i yake ,yawani lumshe ido,ya kwantar d  jikinsa akan kujera.
Cikin sweet voice d'in sa yace kallon ya isa haka yau kika Fara ganinane?"cikin daburcewa ta d'auke kanta had'e da maidasa kan titi tana kalle kalle...
     Babu Wanda yasake mgn acikinsu har suka iso hole d'in da zaa gudanar da partyn atime din anfara Kiran magrib "suna parking ,yadube ta cikin bada order yace ke kijira nayo Sallah tukum sannan ki fito sbd ko kinfito bakison kowaba,raba ido zakiyitayi ,dama gaki bak'auya.... yafad'a had'e da ficewa yarufe motar.


      Cikin jin haushin maganar sa tace ba komai indai wulakanci abin yine"
Koda AK yafita dg motar y'an matan dake Gurin sukayi Masa k'uri da ido(kasancewar baa Fara ba sbd ba duk'a suka isoba ko angon be isoba sbd duk'a yanzun akafara magrib) sun yaba shigarsa ,kowace najin inama inama.
     Ak bedawoba Saida yadauki kusan 20 minit tukum, sannan yadawo Yana wani Shan k'amshi yabude motar beyi mgn ba ,wayarsa tayi ringing , d'agawa yyi sbd ganin angone Hafiz, murmushi yyi had'e da cewa ango ango!yotun yaushe muke anan ?"ku muke jira sbd kasan African time baya cikin tsarina ko?"ohon maka in banzo da itaba so what?"
    Riyanatu kuwa Tasha alwashin muddin bece ta fito ba to bazata fitoba ,zata nuna Masa itama mace ce me daraja..
Shikuwa yacika yyi fam da rainin wayonta sbd ai tunda yabude tasan Yana nufin ta fito shine zata sharesa Dan wulakanci...
Sunkai kusan,6 minit bbu Wanda yabar gun bbu Wanda yyi mgn acikin shi d ita.ak'ule yaduk'a had'e da finciko hannunta.....wani electrical shock sukaji dg shi har it's sbd wannan karon ne farkon da jikinsu ya had'u"cikin jin haushin sa tace mlm sakeni "miye anfanin hakan?"bansaniba !nixaki jawa aji?"haba yarinya ke k'aramar kwaroce wlh yafad'a Yana murmushi Wanda gaba d'aya mutanen dake Gurin tsaye suna jiran isowar ango d amarya suka sahagala d kallon su sbd ganin mugun facewar dasukayi da juna, sannan murmushn da Abdallah yyi azatonsu na sone, yyinda ita Kuma ta galla Masa harara akaro na farko daya kamata k'iri k'iri ta hararesa,yanuna kansa waishi ta d'aga Kai alamar eh"
    Kwafa yyi hade da sakin murmushn mugunta yace Zaki sani yarinya"
Ajiyar zuciya Hafiz yyi da ke kallonsu Yana cikin mota kasancewar yanzun suka iso Gurin idonsa ya haskomasa su..
Murmushi yyi yakama hannun feedo suka fito....Masha ALLAH sunyi kyau tamkar ka sace su ka gudu.
Tafi aka hau yi sbd ganin couples d'in,tuni AK dasuke tsaye tamkar suna firan soyayya yaja RIYAN suka nufi gunsu.

Murmushi RIYAN tayi had'e da cewa Masha ALLAH kunyi kyau"Hafiz yyi dariya had'e da cewa aibamu kaikuba sainaga kunyi tamkar Zara d wata... harara AK ya galla Masa had'e da cewa kana ango kana zuba surutu gsky feedo kiyi Masa fad'a ya canza, yafad'a Yana kallon amarya "
Murmushi tayi batayi mgn ba, sannan suka jera suka Fara tafiya domin shiga holl d'in"yyinda d RIYAN da Abdallah ke bayansu.....

Tuni MC yasaki kid'a guri yarin cabe ,ango da amarya anata musu pics da Kuma video har suka zauna , yyinda wakokin larabawane ke tashi agurin duk y'an matan sun saka jallabiya maza ma jallabiya...

Byn sun zauna RIYAN ta fincike hannunta dg na Abdallah sbd yadda yyi Mata mugun ruk'o na mugunta"har hannunta yyi ja sbd matsa....

Kallonta yyi ido cikin ido yace kin rai naniko?"turo baki tayi had'e da cewa to Ni mai nayine?"murmushn takaici yyi... adedenan mai photo yadaukesu basu saniba.

Sannan yace laifi 2 kenan kin harareni kin turamun Baki"

To kayi hakuri Dan ALLAH ,amma ai...amma what?" Kimayimun shiru ko ki karawa kanki laifi,baki na zaton yanxun kinbar yimun aikiba ko?"

To ai zaa d'aura auren yarjejeniya ,Zaki gane kuranki....haba Mana friend wannan soyewa haka duba ka gani kunyi kyau ,cewar Hafiz Yana Masa rada hade d nuna Masa pic nasu 
shida riyanatu.kasancewar nan take aka wanke photon.

Cikin b'acin rai Abdallah yyi kok'arin karban pic din Amma Hafiz yahana"Yana dariya ya juya gun amaryar sa....


Tab'e baki riyanatu tayi had'e da kallon gefensu batayi mgn ,saidai ta lura duk mutanan Gurin idansu na gunsu itada Abdallah hakan yasa tayi bala'in kama kanta.

Nan aka Fara rarrraba irin cimakar da larabawa keyi ,itadai riyanatu bata ci komaiba gudun kada mutumin nata yace tayi kauyanci...

Dubansa tayi had'e da cewa Dan ALLAH kasaka amaidani gd isha'i tayi  harta wuce ko magrib banyiba"

Banxa yyi Mata"

Dagowa tayi da nufin tasake Masa mgn,sukayi 4 eyes d zeenat ta nufosu a haukace ,jikinta Tasha wasu matsiyatan English wears dasuka fito Mata da suran jiki.

Wani mugun faduwa gaban riyanatu yyi had'e da jin Yana dukan tara Tara.

Saidai Bata nuna wata alamar ta tsorata ba ,ganin zeenat ta kusa xuwa gab dasu yasa ta Kai hannunta cikin na Abdallah, sbd tabata haushi....saurin juyowa yyi da nufin yamata masifa , idanunsa suka hasko Masa Zeenat.


Azabure ta......


Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
    mmn fareesa


Dedicate to all my fans๐Ÿฅฐ๐Ÿฅฐ

Ina mik'a godiya ta ga d'inbin masoya wannan novel ,kunyi ruwan comments a last page๐Ÿ‘๐Ÿป❤

Wannan shafin nakune y'an team din mom๐Ÿ˜‚๐Ÿคฃ๐Ÿคฃ


p15

..... Azabure ta kaiwa riyanatu cafka tana huci had'e da cewa Muna fuka algunguma kasheki zanyi! k'uri da ido Abdallah yyi Mata yaga iya gusunta ga hannun riyanatu cikin nasa... ganin tana kokarin shak'e wuyan riyanatu yyi saurin fisgo riyanatu da k'arfi ta fad'o jikinsa tasaki ka'ra tuni idanuwan mutane suka dawo kansu,tuni Hafiz yamike tsaye... adedenan zeenat cikin b'acin rai tasake kaiwa riyanatu Punch Abdallah yatare had'e da sinketa da wani gigitaccan Mari Yana huci had'e da nunata da yatsa yature riyanatu dg jikinsa..
     Hafiz yyi saurin rirrik'esa Yana tausarsa sbd ganin ransa yab'aci komai zai iya faruwa,yyinda riyanatu ta buya abayansa"
Cikin kuka zeenat ta ce nagode Abdallah sbd wannan banzar ka mareni ,kuna nan kuna cin amanata ,wato har kasaki jiki da ita haka ,inaga ka aureta !to wlh bazaka auretaba zanje na fadawa mom.dole ka rabu da wannan matsiyac.... keeeeeee! Shout up Abdallah ya fad'a cikin hayayyako sannan yace dakikiya !mahaukaciya !inkin cika y'ar halak ki fita arayuwarta....be jira amsarta ba ya finciki hannun riyanatu suka fito dg hol d'in, tuni guard's d'insa suka bud'e musu mota sbd ganin sa azafafe,nan suka bar Gurin.



Acikin hole d'in kuwa sai hayaniya ke tashi da suruttai da yawa nata yiwa zeenat dariya da irin tozarcin da Abdallah yyi Mata suna cewa ALLAH ya k'ara da ya tsink'ata aiyafi dacewa da wadda yazo...

Cike da jin kunya had'e da k'unar rai, zeenat tabar gurin"

Hafiz kuwa girgiza Kai yyi cike da tausayin abokin nasa yace ALLAH shi kyauta.,,,,,,

    ********
Kuka kawai Riyanatu ke yi,tana danasanin yadda da wannan aure"gashi anata ci Mata mutunci harda cewa za'a kasheta.... dallah malama rufemin baki ,matsora ciyar banza miyasa kika nuna kinajin tsoronta?"Koda k'wanji kuka gwada da ita me zata iya yimki?" Mittsss yaja tsaki hade da rufe idonsa...
    Shiru riyanatu tayi tana tunanin magan ganunsa "tabbas bazata sake nunawa zeenat tsoroba tunda ta lura ba son zeenat d'in yakeba mom ce ta tura mishi ita,Kuma tana k'yaleta ne sbd masifar mom da Abdallah...inbaza ki fitaba mumutafi kin yi wani shiru kina tunani" cewar Abdallah yana yatsina fuska....da sauri ta yi ajiyar zuciya had'e da cewa dakai da ita duk banyafe muku ba ,tayi saurin fita dg motar sbd sauri harta mance pos d'in ta.


Cike da mamakin ta Abdallah yace  afili lallai yarinyar nan kin gama rainani wlh ,zankuwa yimiki mugunta son Raina saikiji dadin cewa Baki yafeba...


#########

b'angaren zeenat kuwa cikin  bak'in ciki ta isa gd.ko parking batayi daidai ba ,ta fice ta shiga parlourn mominta hjy ikilima tana kuka mai sauti...afirgice hjy ikilima ta mik'e tayo kanta had'e da rungume ta,tana cewa lfy auta na ? wanene yabata Miki rai ?"shima nasa yab'aci... ABDALLAH Mana !ta fad'a cikin kuka.
     Hjy ikilima tace hmmm narasa miyasa kika mak'alewa matsiyacin yaron nan?"shin dolene kibarsu Mana! dashi da hjy hafsatu wlh zasu gane banida mutunci.....Wai momy daga fa naje gdnsu nemansa sai mom tacemun Yana Gurin party na hafis friend d'in sa,tace naje can nabisa tayima zaton yasanar da ni,nace ah ah,saitamun kwatance.
naje nasameshi da y'ar iskar yarinyar nan.....ta sanar da ita komai....
Whattttttttt?" kina nufin sbd ita yamareki shi Dan iska to wlh yadobo ruwan dafa kansa saina dauki mummunan mataki akansa sbd duk Wanda yaci tuwo Dani miya yasha ,Kuma kema sai kinje da bakinki kin gaya Masa mgn komai Daren dadewa ai hafsatu shashasha ce "iza mai kantu ruwa Zan Mata wlh ,kadama ki sake ki nuna Mata abinda yafaru,kinajina?"
Cikin jin dad'i zeenat tace to momi.,,,,,,,,


๐Ÿ๐Ÿ๐Ÿ๐Ÿ

Masha ALLAH anyi dinner d'in Hafiz lfy inda uban gayyar yaje Amma banda riyanatu"Hafiz kuwa beji dad'i ba..
Washe gari aka d'aura auren sa da fiddausi Ahmed.... Abdallah ya wanku tamkar shine angon,haka akayi hidima lfy akagama lfy , amarya ta tare ad'akinta sai muce ALLAH yabada zaman lfy......


Kamar yadda Abdallah yyi alkawari azuciyarsa zai siyawa su riyanatu gd.cikin ikon ALLAH yacika "komai anxuba aciki d'aki,2 ne sai sitting room d kicin bbu laifi komai yyi daidai mai rufin asiri , sannan yaje da ya'u direba gdnsu RIYAN,sai akayi rashin saa da umma da riyanatu basanan suna wajen sunan k'anwar zuwaira,Kuma atime d'in zuwaira ta shirya itama zata tafi can,ta tsayane sbd masu  siyan abinci ,shine tace su umma suyi gaba.
Cikin mutunci d girmamawa suka gaisa da Abdallah sannan ya bata takardar gd yakuma sanar da ita gobe ya'u direba zaizo yakaisu riyanatu gdn,nan zuwaira tayi ta Masa godiya da saka Masa albarka....
Lokacin da su umma sukaji labari tayi murna da godiya ta kumaji dadin zuwansa Bata nan sbd ita Wai kunya. Riyanatu ma taji dad'i sosai saidai fargabanta Yaya umma da dangin mahaifinta zasuji insunji bayan wata shidda Abdallah yasaketa inya aureta?"""


      Zaune mom take tana tunanin maganar dasukayi da hjy ikilima jiya... Abdallah ya shigo ya aza kansa akan cinyarta yana wani shagwabe fuska... murmushi tayi tace oh my son me Kuma yafaru ne?"
Kallonta yyi yace gsky mom ni gyaran da akayi bemunba kinsan ba d'aki d'aya zamu zauna da itaba gsky"
Yo dama ai dakinta daban na Gefen naka ko?" Ok mom"
yauwa my son abinda nikeso dakai kaga yau sauka 12 days auren nan Kuma da anyisa da 2days za'ayi bikin bud'e campanin ka.
     Cikin k'osawa yace eh"tace yauwa to kada ka yadda in yarinyar nan ta zo wani Abu yashiga tsakaninku da ita ..maana kada ka kusanceta....b'ata fuska yyi hade d cewa habamom! ALLAH ya kiyaye nayi....saikuma yyi shiru cike da jin kunya yana sosa kai" murmushi mom tayi sbd tasan duk miskilancin sa akwai kunya.
Canza topic d'in yyi da cewa yauwa momi kin sanar da su Uncle Suraj kuwa d hajjo ne(mahaifiyar momi) had'e rai tayi had'e da cewa ah ah sbd kasan acikin sirri za'ayi auren ko?"amma su mom ai baidace ace basu saniba tunda shak'ikankine kum....rufemin baki nace bazasu jiba!shiru Abdallah yyi Yana tunanin kan mom d'aya kuwa..muryarta ta katse Masa tunani gun cewa ada nace bazayi lefeba to sai nayi tunanin hakan xaisa agane koba sonta"to yanzun na karb'i kud'i gun abbanka anmata set6 na trolley, bbu laifi ansaka kaya masu tsada kala40 ne andinka 20 .sai dogayen riguna sun isheta sakawa har ku rabu" gobe nema zanbawa hjy ikilima da harira sukaimusu da 50K tayi kunshi ....cikin k'osawa yace hakan yyi had'e da tashi yace mom saina dawo"adawo lfy my son,yace amin had'e da ficewa...


Riyanatu zaune a parlourn su tana kallo tunani take na wannan aure gashi ita rabonta da Abdallah tun ranar da sukaje Gurin arebiant night tamasa rashin kunya k'ila be mantaba yarik'e abun intazo gdnsa yahukuntata...yauwa riyanatu naceba gsky inkinyi aure Zan cewa baffanki ya maidomin bilkisu sbd bbu Dadi Zama ni kadai gsky.
Murmushi tayi had'e da cewa hakane umma,Zama tayi had'e da cewa gsky bbu abinda zancewa yaron nan sai ALLAH yasa yagama da duniya lfy Dan ALLAH kimasa biyayya riyanatu kina gani yasiya mana ya zuba komai na bukata hardasu kayan abinci da fridge  gashi inayin sana'a komai yimuke bamu neman taimakon kowa sai ALLAH!
Murmushi riyanatu tayi  had'e da cewa hakane umma ,Kuma Kinga yace agdnsu zamu zauna kafin yagama namu Kuma be bukatar akaini da komai sai kayan sawa"umma tace eh haka alh bukar yafad'awa dangin babanki yaudai saura kwana 13 ALLAH yasa alkhairi yakaimu lokacin ameen,Amma Wai lfy naga ko sau d'aya baya zuwa fira gunki?" cikin dakiya hade da lalibo abinda zata fad'a tace
Lfy lau umma yyi tafiyane gashi bbu waya guna balle na kirasa, amma yace inyadawo zai siyamun waya.
ALLAH ya maidosa lfy ,tace ameen.

*byn kwana 10*

Abdallah na part d'in sa agefen inda yake motsa jiki,Hafiz ya shigo kamar anje hosa yyi wuri wuri dashi.

kallon sa Abdallah yyi had'e da cewa my man lfy dai ko?"

naga kamar baka lfy ko kuwa angoncin ne yazo da haka?"

Ajiyar zuciya Hafiz yyi had'e da cewa hmmm inafa lfy?"

Fiddausi tunda aka kamun ita Sam tak'i yarda Dani!

Hhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhh๐Ÿคฃ๐Ÿคฃ


Harda rik'e ciki Abdallah sbd dariya bakuma k'amin kyau tamsaba"yyinda Hafiz ya k'ulu iya k'uluwa da iskancin Abdallah.

Abdallah Saida yatsagai ta da dariyar sa tukum yace haba mazaje !yakake haka,yau bbu my feedo sai fiddausi atsaye?

Ina soyayyar dasu bbu d'aga k'afa?kazauna tausayinta kome yasa ka kasa biyan bukatarka gaka da fitina ,aini nazata an rugada an wuce wuri....dallah dakata  ba dariya nazo kamunba "zaka wani tasani gaba kanayi harda rik'e ciki ,kabani shawara ya zanyi pls?"

Tabe baki Abdallah yyi had'e da cewa abinda zakayi yawuce ka yi Mata ta k'arfi ko kasa Mata k'wayoyi a drink feeling yataso Mata....

Girgiza Kai Hafiz yyi had'e da cewa duka bazan iya ko d'aya ba.

Tsaki abdallah yaja had'e da cewa to shikenan ka kashe kanka sbd son mace da tausayinta "

Hafiz yace hmmm dole kace haka tunda baka fad'a tarkon SO ba"

Yatsina fuska yyi hade da cewa bana fatan na fad'a kuwa"

ga shawara ta karshe in za iya?"

Zan iya Mana"

Kaje kayi Mata barazanar k'ara aure ,zata yadda da Kai inhar tana sonka...amma kuma....hmmm amma what?

Inbazaka iyaba kaikasani"

Shiru Hafiz yyi...can yace to bara na kwada mugani.

Towai miyasa ma bata yarda dakai?"ko maitar ka ka fito fili ka nuna Mata.

Cikin jin haushi Hafiz yace rufemin kofa fa take...tsaki abdallah yaja had'e da cewa sai kace ba nmj ba " wlh in nine ta karfin tsiya Zan Mata tunda na biya sadakina.

Murmushi Hafiz yyi had'e da cewa to shikenan sai kabari in RIYAN ta Zama mallakarka kayi hakan... mitttsss ALLAH ya kiyaye,aikasan auren dazamuyi ko?"inma kayi wannan tunanin to kabari,sbd nafi k'arfin hakan...

Girgiza Kai Hafiz yyi had'e da cewa ai saura 3 days ko ?" Dukda kace baza ayi komai ba na fad'a wa manyan abokanmu.


Kaikasani yanxun kaje gun matar ALLAH yabada saa kayi kok'ari kasama Mana baby,cewar Abdallah yana dariya.

Tsaki Hafiz yyi had'e da cewa Zan rama sannan ya fice...

Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


   Story& written by
       mmn fareesa

Dedicate to Queen❤


 naji wasu maganganu gameda wancan novel d'in nawa (WATAH UWAH) wasu na cewa na siyarwane,wasuma anfara siyarmusu...
To inaso kusani duk makirar data siyarmun da novel ALLAH ya isa banyafeba.
Sannan inaso kusani ni mmn fareesa nafi k'arfin insaida novel a social media๐Ÿคท๐Ÿผ‍♀


    p16

""""Hafis ne tsaye kofar gdnsu RIYAN Yana jiran zuwan ta kasancewar yatura akirata."kwalin wayane ahannunsa daya siya Mata da layi da komai"
Ak'alla kud'in wayar sunkai 50K" yyi seving d'in contact na Abdallah aciki.
    Tunani yake azuciyarsa sbd yanaso ya nunawa RIYAN Abdallah ne yasiya mata wayar shin zata karb'a ko kuwa?" Salamu alaikum....sallamar RIYAN ta katse Masa tunani..
    Cikin  sakin fuska had'e da mamakin ganinsa tace ahhh yah Hafiz Kaine agdnmu ?"murmushi yyi had'e da cewa aikuwa !badolena ba nazo sbd mijinki ya matsamun nakawo Miki wannan, kinsan in yanajin sarautar tasa sai ahankali"yafad'a Yana mik'a Mata kwalin wayar....
     Hararar wayar tayi had'e da cewa gsky kamayar Masa da abinsa...haba! RIYAN hakan be kamataba"kinsan bbu kyau ayimaka kyauta kamayar ,sai shaid'an ke hakan ,sai kace bakya zuwa islamiya ne!cewar Hafiz fuskarsa na nuna beji dad'i ba...karb'a tayi  sbd ganin beji dad'i ba"ahankali tace shikenan nagode Amma waya nuna maka gdn?
Murmushi Hafiz yyi had'e da cewa ya'u direba ne.
To nagode sosai agaidamun da amarya,insha ALLAH zataji...yauwa  yace ki kirasa number insa na ciki,yatsina fuska tayi had'e da cewa yo miye Kuma abin nakirasa?"yamin me ?". haba RIYAN !nifa banason kina haka,kisani duk aure , aurene bbu wani batun kice ai auren yarjejeniya sbd musulunci be yadda dashiba,sbd haka in anyi auren nan ki zauna da abokina da zuciya d'aya... ajiyar zuciya tayi cike da gamsuwa tace to nagode sosai"
Sannan sukayi sallama tayi cikin gd da kwalin wayar ahannunta.,,,,,

Umma dake zaune kan kujera ta na dame wani abu cikin cup gefe ga gwangwanin Madara peak emty ,ta dubi RIYAN ta ce kindawone?"
Eh umma ,Kinga Abdallah ne yabani "yace agaidaki Wai kunya yakeji bazai shigoba(tayi k'arya)
Murmushi umma ta yi hade da cewa to ba komai Ina amsawa, sannan ta karb'i wayar tana dubawa had'e da yiwa RIYAN fatan alkhairi."
Ajiye wayar umma tayi had'e da maikawa RIYAN cup din tace ungo maza shanye kiban cup d'in"bbu musu ta karb'a tashanye tana tandar baki sbd jin dadin maganin...
       byn ta shanye ne ,umma ta jawo wata kula had'e da cewa riyan maza ki cinye naman nan ,Amma banda K'ashi, d'azun zuwaira ta kawosa kina bacci...turo baki tayi had'e da cewa Dan ALLAH umma kibarsa wlh bbu dad'i sai d'aci ,garama me dad'in nan yafi wlh... hararar ta umma tayi had'e da cewa maza kicinye yanxun"badan tasoba taita turawa tana mamakin miyasa ake Bata wad'an nan abubuwan?";;;


        ******
Abdallah ne zaune a parlourn sa fuskarsa atamke sai tsaki daya keta yawan ja"sbd daya tuna gobe zaa d'aura auren sa da wannan yarinyar bacin ba itace choice d'insa ba....wayarsa tayi ringing yaduba yaga bakuwar number...tsaki yaja had'e k'in d'agawa....sake Kira akayi,ak'ule ya daga bbu ko sallama yafara masifa kamar haka!dallah wanene zaka takuramun ne?"bacin banida lokacin kowa e ye? 
 cike da mamakin sa Riyan tace hmmm nice RIYAN , sannan kai kace nakiraka da mazan kiraba!what kinada hankali kuwa? wane makaryacin yafad'a Miki hakan ne Wai?"lallai kin waye  
tunda har kin Fara rik'e China phone shine kikasamu contact d'ina kika kirani kinunamun kin waye ko?"
To bara kiji last warning duk inkika sake kirana should be in trouble".... yafad'a Yana mugun sakin doguwar tsuka yakashe wayar had'e da dafe kansa....haba Mana AK inata mgn kana zuba masifa lfy dai ko?"cewar Hafiz daya shigo yanzun "kallon sa Abdallah yyi off & down sannan yace hmmm dg gani kashiga dg ciki sbd gashi ka canxa"look mlm ka amsamun tambayata ba wani zaurance zakamunba"tabe baki Abdallah yyi had'e da cewa wannan yarinyar ce sbd sokwanci ta kirani.... yafad'a Masa abinda tace....

Hhhhhhhhhhhhhhhhhhh๐Ÿคฃ๐Ÿคฃ nine nan na had'a komai"

Kana nufin Kai kace nace ta kirani?"

Yes"cewar Hafiz Yana d'aga gira"

Azabure Abdallah ya mik'e had'e da cewa wlh ka gama Dani ,kazubar min da aji, to kamayi gaggawar zuwa ka fad'a Mata k'arya kake ,sbd kadama ta dauka nadamu da itane,nikuma kasan nafi k'arfin hakan....hmm AK kenan ba'asan inda Rana ke faduwa ba, kabi ahankali , sannan Ni ba wannan yakawoniba ,nazone inmaka godiya sbd brain Inka naja shawararka tayi amfani nida my feedo mun jone..sannan in sanar da Kai  cewa gobe byn angama d'aura auren ka ,nashiryawa abokanmu walima ....ka gama?" cewar Abdallah cikin fushi" eh wlh nagama "bara na wuce my feedo na jirana naje muci gaba dg inda muka tsaya,cewar Hafiz cike da tsokana.... mitttsss Abdallah yaja tsaki hade da barin parlourn"
   Girgiza Kai Hafiz yyi had'e da ficewa.


    ########
Riyanatu zaune da dare tana hawaye had'e da kallon d'akin datake aciki sbd dg yau bazata sake kwanaba sai tsawon wata 6"wani gefen Kuma tanajin bak'in ciki akan maganganun da Abdallah yafad'a Mata d'azun,"
anya batayi kuskuren amincewa da wannan aurenba,gashi bbu Wanda yasani dg ita sai iyayen Abdallah dashi"ga Fatima na a skul balle tasanar da ita suyi shawara "ALLAH dai yakawo  Mata mafita zata dage da addua "
Kwanciya tayi tana tunanin irin zaman da zatayi da Abdallah da mom...har bacci yyi gaba da ita...


Masha ALLAH Rana Bata k'arya saidai uwar d'iya taji kunya "ayau aka d'aura auren ABDALLAH Kabir girma da RIYANATU umar mohd a masallacin dake  G R A nassarawa... yyinda ango bejeba yarufe kansa adaki yaki fitowa...shikuwa Hafiz tamkar shine angon sbd yadda nan nan da mutane.

Byn antashi sg daurin auren da ba'yi taroba sosai , Hafiz ya je da abokansu gdnsa akayi walima, sannan aka watse,Hafiz yanufi gidansu AK...

Part d'in mom yafara zuwa....kafin yyi sallama yaji mom tana cewa to hjy ikilima haka za'ayi goben da wuri zamu tafi muyi sakko Aina fad'a Miki dole....ah kamar mutum ko?"da sauri Hafiz yyi sallama had'e da gaidasu,fuska atamke mom ta amsa atakaice,cikin ladabi yace mom an d'aura AURE! ALLAH yasa alkhairi....kaga dakata ba aminba wlh mitttsss jeka tunda mun gaisa inkuma gun Abdallah kazo jeka sashensa kasamesa.


Hafis bece komaiba ya fice, azuciyarsa Yana musu adduar shiriya..

Ankai ruwa Rana tsanin Abdallah da Hafiz akan dole Abdallah ya shirya yasaka manyan kaya sbd shi angone.

Saida hafis ya nuna yyi fushi sosai sannan ya saka.

Wayyo ALLAH zanso inga mai karatu ,ya kiyasta azuciyarsa yadda Abdallah yyi masifar kyau sbd kayan sunyi mugun karb'arsa"


Milk shaddace ajikinsa Tasha aiki da brawn zare ,ga hula da takalmi duk brawn yasaka ,sai fitinan nan kamshi ketashi ajikinsa.


Tare suka fito shida Hafiz ,saidai fuskarsa atamke take"

Inda abokansu suke suka nufa..


Karfe 8:12 pm su mama zuwaira da dangin uban RIYAN sai wasu abokan arziki,suka iso gdn Alh Kabir girma da amarya RIYAN dake kuka tana a lullub'e yyinda wasu kwta gud'a.

Directly part d'in mom su mama zuwaira suka nufa da RIYAN sbd akaita Amana.


Sallama sukayi.....


Share pls

BY 
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



   Story & written by
   mmn fareesa



p17

 ...... Sallama sukayi kafin su shiga ciki"mom da hjy ikilima dake hakimce kan kujera center table na gabansu d'auke da kayan motsa Baki"cikin kak'aro murmushi suka amsa sallamar ,mom ta mik'e ta kamo hannun RIYAN dake lullub'e ta zaunar da ita kusada ita"
Cikin iya  bariki hjy ikilima ta musu maraba , sannan suka gaisa had'e da bada amanar riyan ga su mom.
Cikin dariyar yak'e mom tace hmmm ba komai ai y'armu ce kunji"zamu kula da ita insha ALLAH.
   Riyan ta girgiza Kai sbd ganin yadda mom keyi  azuciyarta tace hmmm lallai matan nan shu'umai ne na gske...cikin sakin fuska sukayi sallama dasu mom ,wadda duk dangin uban RIYAN nata yabonta suna tadace suruka dakuma gd aljannar duniya..lolx..
Part d'in Abdallah suka nufa da ita" kowa yaba kyan gdn yake had'e da santinsa , yyinda riyanatu gabanta ke faduwa,byn sun k'ara Mata nasiha su mama zuwaira da goggunanta dasukaxo dg k'auye sukayi sallama,sukabar RIYAN na kukan rabuwa da ummanta dakuma tausayin kanta...


     Tsaye take ta jingina da motar ta parking space na gdnsu Abdallah"hawaye ne masu zafi ke zuba a kumatunta,har cikin ranta tasan tana masifar son Abdallah da kishinsa ,saidai data tuna irin wulakancin da cin fuskar dayayi Mata sai taji wani irin bak'in ciki arayuwarta. rabonta da gdn tun ranar da Abdallah ya mareta sai yau,gashi jiya dataji firar momynta da mom sunayi ta tsaya Mata arai"
Shin tasanar da Abdallah ko kuwa?"to yanxun inhar tasanar da shi ta tabbata marar zuciya kenan kamar yadda yace?"
Wai tsayuwar me kike kinyi shiru?" Muje da ALLAH lokaci natafi,dare yayi,cewar hjy ikilima tana shigewa cikin motar..
Ajiyar zuciya zeenat tayi had'e da shiga ciki ta tada motar zuciyarta bbu dad'i Dan jitake azuciyarta Abdallah nason Riyanatu....iska na wahal da me kayan Kara wlh "gwarama kin hakura da shegen yaron nan shizai fimiki sauki "sbd ko a da abinda yasa nikeso ki auresa shine dukiyarsa da Kuma muma muyi suna,to Kuma ayanxun bbu wannan na canxa shawara ,Amma fa hardani amasu cin dukiyarsa."sannan yaron nan ya wulakantaki agaban bainar jamaa,Kuma nima bayason taronmu da uwarsa Kinga kuwa dole na dauki mataki akansa ,byn nagama sannan mugaya Masa mgn...
Ahankali zeenat tace wlh momy narasa miyasa sonsa yaki fita dg Raina?"
Tsaki hjy ikilima ta ja had'e da cewa aisai kiyitayi,ke inhar kinsan ciwon kanki  kyace kina sonsa duk tozarcin da yyimiki...Amma mom ki....rufemin baki,ta fad'a cikin tsawa.
Tsit zeenat tayi batasa ke mgn ba har suka iso gd.

   **********
Bangaren Abdallah kuwa Gurin karfe 9:23 pm yanufi part d'in sa fuskarnan tasa a tamke ,Abu 2 kecimasa rai na farko wannan aure, dayake ma kallon na dole dakuma ma  kalmar da riyannta fad'a Masa Wai dg shi har zeenat Bata yafe musuba , shiyasa yazo yanxun yymata abinda zatace Bata yafe d'inba d hujja..
Straight bed room d'in riyan yanufa..
    Bbu sallama ya murd'a kofar yashiga...riyan dake zaune a tsakkiyar gadonta fuskarta Duke tana hawaye taji anshigo.... k'amshin turarensa yasa tagane shine...wani irin faduwa gaban ta yyi ,batad'ago ba tajira  jin dame yazo ne?"
Keeeeeeeeee! yafad'a cikin kakkausar murya"tashi ki had'a mun ruwan wanka ,Inna fito akwai kaya ajike a toilet ki wankemun sannan kishiryamun kayan guga daaka kamun a wardrobe...
Yafad'a cikin tsawa had'e da cewa kobakya jine?"


Wani irin bak'in ciki had'e da k'unar rai, riyanatu ta ji azuciyarta"

Sbd ganin yadda Abdallah ke juyata tamkar wata baiwarsa"ahankali ta d'ago kanta tagansa yakafe ta da sexy eyes nasa Yana hararan ta.
Saurin janye idanunta tayi had'e da cewa gsky kayi hakuri dare yyi sannan Kuma dg xuwana...shout up your mouth,kin isa Ina mgn kinayi" ok kina nufin bazakiyiba?" To bara kiji bauta kikazo kiyimun kafin adadin kwanakinki su k'are a gdn nan,ko kinmanta kince Baki yafemunba  to yanxun Zan Fara Miki abinda nagada ma saikice baki yafeba d hujja,Zaki tashi ko kuwa stupid ko anfada Miki dama zama aka auroki kiyine?"to inkinma yi tunanin hakan kiyi saurin canxawa,Zaki tashi ko kuwa?"
Hawaye masu zafi nata zuba a baby face nata ta fice, yyinda d Abdallah ya rakata da harara..

     Byn ta had'a Masa ruwan wankan, sannan ta fito tafara shiryamasa kayan a wardrobe.
Sai share hawaye take tana tunanin ummanta...ana hakan Abdallah ya shigo ya matso dab da ita....tuni jikinta ya kama rawa" tsaki yaja had'e da dukawa ya dauki jallabiya,yanufi toilet...
Byn minti25
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
   Mmn fareesa


p 18

Byn minti25 riyan ta gama shirya kayan sai hak'i da nishi take sbd kayan nada yawa"
Bed room d'in ta ta koma domin tajira yafito yashirya saita koma"wayarta ta jawo ta Fara game,wani gefen zuciyarta natuna  nin gd,dakuma rayuwar da zatayi awannan gidan...takai kusan 20 minit tukum ta ji wani mahaukacin Knocking"girgiza Kai tayi had'e da tashi ta bud'e...wani sanyayyan k'amshi yadaki hancinta,talumshe ido"atsawace yace keeeee!dg yau nasake fad'a Miki mgn ko Baki umarni ,ki ka bari nakoma maimaita Miki Zan nuna Miki colour Dina"stupid!kallonsa tayi acikin second 6,sanye yake da Fara k'ar din jallabiya,datayi bala'in karban sa yyi kyau ita kanta RIYAN tace Masha ALLAH"
Tsaki yaja akaro na 2 sannan ya juya tabi bayansa zuciyarta bbu dad'i sbd irin wulakancin da Abdallah ke Mata.,,,

    Yana shiga gefen bed yazauna had'e da Fara duba lop top"RIYAN data shigo ta ajiye wayarta gefen bed ta shiga toilet"
Ajik'e cikin bucket ta Sami kayan , fararen vest ne da jallabiya kusan kala4 ajike, zuciyarta na zafi tana kuka tana wankin sbd wannan ne karon farko data wanke kayan nmj a rayuwarta"dubawa tayi taga bbu boxers aciki,takuma yi alk'awari inhar akwai bazata wankesu ba ko zai kasheta wlh"...ta d'au lokaci kafin ta gama ta shanyasu a toilet d'in"
Abdallah kuwa yajima yanata aikinsa can wayar riyan ta Fara ringing bbu k'akk'autawa,tunbe kulaba har yafara tsaki sbd k'aran na damunsa"kallon agogon dake jikin bango yyi yaga 10:34 pm,tsaki yaja had'e da cewa miye abin Kiran amarya a irin wannan time din?"inbacin son jin gulma... mik'ewa yyi da nufin kashe wayar,wani Kiran yakoma shigo,Yadubi fuskar wayar yaga ansaka Y'AR SIT"yatsina fuska yyi hade da cewa gsky yarinyar nan muguwar y'ar kauyece to inba rashin class ba meye nasaka wani y'ar sit mitttsss"
daukar wayar yyi yashiga contact...by surprise yaga tayi seving number insa da Mr arrogant.๐Ÿ˜ณ

Adede nan riyan ta fito dg toilet idanunta sunyi jajir sbd kuka"wani mugun faduwa gaban ta yyi sbd ganin wayarta a hannunsa, tunani take ALLAH yasa bega....keeeeee!zonan ,da sauri ta dubesa taga fuskarsa murtuk bbu alamar wasa aciki kinta Dan ALLAH kayi hakuri wlh mistake n.....nace kinmun wani abune?
Tambayar ki zanyi kawai"yafad'a batare da yakalleta ba"wanne suna kikayi seving number d'ina dashi?

Ummm....dama..dama,ban... shout up"lallai RIYAN kingama rainani ko?Amma bbu damuwa,saidai kin jahilci Abdallah Kuma har yanzun bakisan ko waye Abdallah ba"sannan Zaki cigaba da ganina ayadda kika d'aukeni"
And last nayi seezing wannan China phone d'in naki....turo baki tayi had'e da cewa to dama kaika siyamun Kuma baninace abaniba...

Dariya yyi had'e da kallon ta up & dawn , yyinda ita Kuma ta shagala da kallonsa sbd ganin yadda yyi mugun kyau...ni Abdallah nafi k'arfin hakan inma fad'a Miki ,Wanda yabaki shiya siyamiki wayar, sannan zanmiki hukunci sbd naga kin rainani and last ki gyaramun bed sannan ki had'a mun cofee,innayi bacci kya iya tafiya ki kwanta da 7:am tayi nasameki a parlou na...

Cike da mamaki riyan ke dubansa "

Kafin tace Ni ban iya had'a coffee ba , sannan bazan iya tsayawa ba har kayi bacciba a irin wannan lokacin sbd shed'an"

What?" Mekike nufi da hakan?

Turo baki tayi had'e da cewa kagane Mana"

Tabe baki yyi had'e da cewa"inhar kikasake turomun k'azamin bakinkin daya ke warin kuka da daddawa zanbaki mamaki..ke yanxun dakike cewa shaid'an yoke har kinkai mace?dubeki kwaila dake mittsss yaja tsaki hade da cewa"

Kije ki yi abinda nace banason surutu"

Bata kulasa ta Fara gyaran bed d'in Wanda bbu abinda yyi and yawal da itane ,ga hawaye nata zuba a kumatunta , gwanin ban tausayi...

Byn ta idar ta zauna k'asa kan carpet ta cigaba da kuka.

Dagowa yyi sbd jin wayarsa na ringing yaduba yaga Hafiz ne,tsaki yaja had'e da cewa ke dauko wancan basket d'in nafad'a Miki, yadda zakiyi"

Mamaki riyan ke yi,wato Yama iya hadawa sbd yawahal d ita zai ce ta had'a"

Bbu musu ta d'auko Yana Jan ajinsa da Shan k'amshinsa har yagama fad'a Mata,byn ta had'a ta Kai gabansa ta aje.

Ta juya tanufi kofar fita ,bece komaiba ya k'yaleta...

Koda ta koma d'akin,wanka tayi had'e da alwarla tayi nafila,ta dad'e ta addua akan ALLAH ya Bata ikon hakuri da juriya da Abdallah da mom tukum ta kwanta tana tunane tunane har bacci yyi gaba da ita...

********
Washe gari tunda wuri riyanatu tayi wanka da salla ta nufi parlourn  Abdallah ta Fara gyaran parlourn... Abdallah nashigowa  yasameta tana aikin,,dawowarsa kenan dg masjid sbd yau yatsaya yyi karatun alk'ur ani mai girma.

Kallonta yyi,da sauri ta duk'a had'e da cewa ina kwana?"

Ayatsine yace lfy?"

Jiyayi tabashi tausayi sbd ganin tun kafin7 d'in ta Fara aikin"Kuma yalura idanunta sun kumbura.


Wanka zanyi"yafad'a tamkar bayason mgn"

Da sauri ta tashi ta shiga ciki tabassa a parlourn.

Saida ta wanke toilet d'in tukum ta had'a Masa ruwan wanka kafin ta fito tasoma gyaran room d'in.

Tana ciki yashigo yanufi toilet,byn ta ida ta fito Masa da manyan kaya sbd tafi ganin sunfi Masa kyau duk da tana gudun kada yadisgata.

Parlourn ta koma ta zauna.

Shikuwa Abdallah byn yafito yagama shafe shafensa, yaduba kaya yaga milk shadda y'ar ciki da malun malun...tsaki yaja had'e da cewa Wai miyasa RIYAN kin rainani ne?"

Dg shi sai vest da boxe ya murdo kofar...da sauri riyanatu ta d'ago kanta suka had'a ido da Abdallah... harara ya aiko mata da ita had'e da cewa zakixo ki canxamun wasu ko kuwa?

Atsorace ta kauda Kai sbd ganin irin shigar dke jikinsa,shikanshi yalura da hakan ,sai ya tab'e baki yakoma ciki.

Binsa tayi had'e da cewa Dan ALLAH kayi hakuri kasakasun ,anjima seka canxa yanxun kafin na canxo wasu lokaci yatafi gashi hjy ta Aiko kiranka....

Mittsss dallah naji Zaki iya tafiya ko"

Batace ko maiba tajuya ta fice.

Tana nan jiran fitowarsa yyi break fast,ya fito yyi masifar kyau ,sak yafito a angonsa lol.x..

Fuska daure yace keeeeeee!dallah zonan ki dauramun link na maballin tunda kece kikaja nasakasu, yafad'a na Jan doguwar tsuka.

Girgiza Kai tayi had'e d tashi ,jikinta na rawa sbd tsoron hannu zai taba jikinsa dukda tasan mijintane Amma ai basa son juna Kuma ba aurene na dindin ba.

Ahankali ta Fara saka Masa,dukda hannunta na kirma,shikuwa hankalinsa na gun waya Yana dubawa Yana murmushi..kawai yaga hasken flasha ...da sauri yad'ago sukayi 4 eyes da Hafiz .

Murmushi Hafiz yyi had'e dayin sallama yashigo Yana cewa ango ango!!

Hararar d Abdallah Masa yasakashi yinshiru,mlm inkasan photo ne kama na wlh kama yi saurin gogeshi ko nahada maka borm Gurin feedo ince kanada budurwa...


Dariya Hafiz yyi had'e da cewa hmmm to saime inkace hakan?"

Ina kwana yah Hafiz cewar RIYAN,byn ta ida gama aikinta.

Lfy lau amaryar mu, Masha ALLAH kunyi kyau wl....ke had'a mun tea dallah"

Bata ce komai ba ta had'a Masa, sannan ta zauna tajira ,sai zolayanta Hafiz keyi Bata kulasa sbd ganin yadda Abdallah ke hararanta.

Byn yagama break fast ,suka fito da ita harda Hafis domin suje su gaida Abba d mom.

Parlourn abb

Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by mmn fareesa


  p19

Parlourn Abba suka yi straight"Abdallah ya Fara sallama yashiga , sannan su riyan d Hafiz suka mara Masa baya"
   Zaune Abba yake yana duba jarida, yyinda tire babba agabansa  da alamar bejima da yin break fast ba"byn ya amsa sallamar ya aje jaridar ya d'ago kansa.....atare gaban Abba Dana RIYAN yafad'i.
Dasuka had'a ido,saurin duk'awa tayi ta gaidashi cikin girmama wa,shima Hafiz haka , yyinda da gogan ya matsa jikin abban Yana shagwaba... murmushi Abba yyi hade da kallon RIYAN yace y'ata kiyi Masa fad'a ya Dena wannan shagwab'ar bacin yagirm....haba Abba! Kada kajama yarinya ta rainani wlh"yafad'a Yana wurgowa riyan harara...
Kauda kanta tayi had'e da dukar k'asa"hararar sa Abba yyi hade da cewa banason haka fa ,kadena kanajina?"cike da girmamawa yace eh Abba kayi hakuri"murmushi yyi had'e da cewa ba komai , yasunan y'ar tawane?"kallon tambaya Abdallah keyiwa Abba. Sbd yalura kamar son aurenma Abba yake...sunanta RIYANATU Abba! muryar Hafiz ta katse Masa tunani"
   Masha ALLAH"kiyita hakuri kinji y'ata" ALLAH yyi muku albarka. suka amsa d ameen banda Abdallah daya Lula tunani...
Tashi Hafiz yyi had'e dayiwa Abba sallama ,itama RIYAN cike da jin kunya tace Abba sai anjima,amsawa Abba yyi Yana murmushi haka nan yaji Yana son yarinyar Kuma bayason tarabu da Abdallah...
Abdallah yace Abba bara muje part d'in mom mugaisheta" murmushi Abba yyi hade da cewa to...

Koda suka fito da niyar shiga parlourn momin...kawai suka yi clash da ita d hjy ikilima"sunsha wanka cikin shiga ta alfarma ko waccensu Tasha las babba sai kamshi suke"kicin kicin da fuska Abdallah yyi sbd ganin mom tare d hjy ikilima.  yyinda riyanatu kejin   faduwar gaba, shikuwa hafis duk'ar da Kai yyi"
My son lfy dai ko?" naganku atare da yarinyar nan ko"tab'e baki Abdallah yyi had'e da cewa gaisheshi ki mukazo yi....Dan zaka zo gaisheni saikamun gayyane .... mittsss cewar mom cikin tsawa.... murmushin takaici Hafiz yyi had'e da cewa Ina kwananku mom? bejira amsarsuba yyi gaba yajira Abdallah sbd yasan sbd shi mom ke masifa"
Mom ta dubi riyanatu dake gaidasu awulak'ance kafin tace last warning zanbaki kada nakoma ganin kina binsa inzai tafi wani guri inba da izininaba,Zaki b'ace mun da gani ko kuwa"sum sum sum riyan ta bar gun.

     Tsaki mom tayi had'e da maido kallonta ga Abdallah ta hararesa" adole yaduni hjy ikilima dake kallon sa yace momi Ina kwana?"
Tab'e baki tayi had'e da cewa hmmm lfy qlau "ai nad'auka bazaka gaidaniba ai"banza yyi Mata,saima ya dubi mom ya sassauta murya yace mom Ina Zaki da safen nan?"
Eh..umm ...Zan tafine,Gurin gaisuwa"waya rasune?"Wai miye haka Abdallah ko turkeni zakayine da tambaya??
Ko ubanka bemun haka balle Kai"inzakamun addua kayi inbaza kayiba nidai natafi...ta fad'a tana tafiya, yyinda hjy ikilima ta mara Mata baya"
Girgiza Kai Abdallah yyi,ransa bbu dad'i,ya nufi campaund na gdn sbd yasan Hafiz bewuce can...

      ********
Riyan ce zaune kan kujera,a waiting parlour na Abdallah" sai tunanin ummanta take gashi Abdallah ya karb'e wayar balle ta kirata" sbd itama yanxun tanada waya...kee!tashi kihadamun ruwan wanka"da sauri ta juyo suka had'a ido tsaki yaja had'e da cewa banhanaki kallonaba!
Tashi tayi cikin sanyin murya tace Kai ya akayi idonka yakalli nawa har kasan Ina kallonka?"Amma kayi hakuri"
What?"zonan ! yafad'a Yana nuna kansa had'e da tunkararta....da gudu ta shige bed room d'in sa ta rufe,Dan duk azatonta dukanta zaiyi....ruwan wanka ta had'a Masa kafin ta lek'o ta kafar mukulli taga baya parlourn"da sauri ta fito dg d'akin... adedenan cikin ma'aikatan mom wata zulfa"tabiyosa da ture da kayan abinci asama, da alama lunch ne aciki"da sauri ta yi wuf tashige bed nata...ko inda take be kallaba,amma hak'e yake da ita"

Kan dining area ta aje"kokarin wucewa take , idanunta su hasko agogan Abdallah mai tsada da ke bisa ya manta  d'azun...da sauri ta dauka ta sake a siket nata....ki tura sosai sbd tad'an lek'o....cewar Abdallah ke kallon duk abinda take.....wani mugun faduwa gaban ta yyi had'e dajin mugun tsoro tasan yau zamanta ya kare agdn muddin mom tasani dukda Bata gd....jiki na kirma tace Dan ALLAH kayi h.... shout up!ya fad'a atsawace had'e da cewa on your kneel! da sauri tayi, atsawace yace and hands up"
Babu musu ta yi tana kuka tana Masa magiya,cike da tsana yajuya  yanufi bed room d'in sa Yana cewa kijirani kinji RAT"

Xufta tagaji iya gajiya ga tsoron kada akoreta kuma wannan karon ne n afarko datayi sata arayuwarta ,gashi ankamata Kuma tayi nadama,sbd dolece tasakata yin sata,tanemi taimakon mom akan za'ama mamanta aiki ,saita zageta tas tak'i Bata kud'in harma tana cewa zata koreta"
Hakan yasa tayi sata kota samu kudin....lfy dai ko zulfa naganki ahaka?" Cewar RIYAN dake waige waige gudun kada mutumin nata yafito....tas zulfa tasanar da ita abinda tayi dakuma dalilinta dayasa tayin"cikin kuka tace Dan ALLAH kibasa hakuri"kafin RIYAN tayi mgn k'amshin turaren Abdallah ya daki hancinta"
Da sauri ta duk'a had'e da cewa Dan ALLAH kayi hakuri akan laifin da zulf... you are very stupit kin isa kisa nayi abinda banyi niyaba ,kinsan dama kinmun laifi d'azun ko?"shine yanxun zakimun shishshigi da katsalandan dan haka maza kiyi joining da ita"

Hawaye na zuba a fuskar zulfa tace Dan ALLAH kayi hakuri ka saurareni kada laifina yasha feta...

Banza yyi Mata yyi musu ,saima ya zauna yakunna laptop ya aza kan center table, yyinda riyanatu batace komaiba ta yi joining din zulfa kamar yadda yace suka cigaba da knee &hands up.

Yakai kusan minti 20 kafin ya bar lop top d'in  da wayoyinsa,ya fita waje"

Da sauri riyan ta tashi ta lallab'a ta dauki wayar ,kasan cewar baa security takeba sbd saka waya a security baya a tsarinsa.

"Number din umma ta saka had'e da Kira"

Bugu2 umma ta daga ,cikin murna had'e da boye damuwarta suka gaisa da umma"sannan umma ta ce ,nakiraki d'azun wayar akashe aketa cemun"

Da sauri riyan ta ce eh umma"tasamu matsala ne,Amma Zan canza wata"(tayi k'arya)

Dama Dan insanar dake gobe zanje k'auye insha ALLAH Zan kwana 2 kafin nadawo daganan ma mudawo da bilkisu...

Kai umma dan ALLAH ,Amma kinzo muyi sallama ko?"

Bakida hankali yarinyar nan wlh"nazo nayi me agdnki?

Kidai gaidamun Abdallaan kinji,yaron nan baya gajiya da d'awainiya ai d'azun yazo yagaidani da yaron nan Hafiz abokinsa...

Lah umma Ashe kunga juna kedashi?

Nasan bakyason yaganki"

Murmushi umma tayi tace hakane"Amma ko yau din wlh bankallesaba har yagaidani na amsa kaina na duk'e...Kai gsky umma kunyarki tayi yawa...hmmm riyanatu ALLAH ya shiryaminke"yanxun da wayar waye kika kirani ne?

Eh umma wayarsa ce"oh ni bintu"to sai anjima...lah umma kijira...d'it ta yanke wayar...

Murmushi RIYAN tayi had'e da cewa Kai umma wlh kunyarki tayi yawa"ta fad'a tana kokarin goge number in ta maida wayar taji ance inkin   gama bani wayar....

Share pls

BY 
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by 
mmn fareesa

Dedicate to all my fans๐Ÿ˜ป๐Ÿ˜ป

Not edited

  p20

"""Arazane ta d'ago kanta tagansa tsaye yakafeta da sexy eyes nasa"fuskarsa murtuk bbu alamar wasa acikinta.
Cikin faduwar gaba had'e da daburcewa tayi saurin aje wayar a inda ta d'auka"murya araunane tamkar za tayi kuka tafara mgn"kayi hakuri Dan ALLAH ai kaineka kwace way... d'aga Mata hannu yyi alamar beson ji, sannan yyimata alamar tazo "magiya tahauyi dabasa hkri. yyinda yyimata banza saima Zama yyi, had'e da yiwa zulfa alamar ta zo kusadashi,ita kuwa ta galabaita da kneeling down gakuma hands up"
 Da k'yar take tafiya har ta iso gabansa ta duk'a tana kuka"yakai kusan minti2 kafin yakalleta yace meyasa kikayi sata?"
Cikin kuka tahau basa dalilinta" kije Zan bincika"yafad'a atakaice, yyinda yake kallon RIYAN ta wutsiyar ido dake Shirin guduwa,sbd dama ta tsayane taga zai k'yale zulfa kozai Mata rashin m ne.....tashi zulfa tayi ta fice"inhar kika koma guduwa kinjawa kanki"garama kizozai fi Miki sauk'i".....tsaye tayi tanata zare ido ,wata zuciyar tace gara kitafi kawai zaifi miki.cikin sand'a take tafiya har ta iso gabansa "ta wani murgud'a baki tukum tace gani"yakai kusan minti 4 kafin yadako yadubeta  ya yatsina fuska yace gsky naga k'ok'arin ki kina under purnishment kina k'arama kanki laifi"Aina fad'a Miki kika koma murgud'a min bakinki me warin kuka da daddawa zanbaki mamaki,to zanbaki mamakin...by suy taji lallausan tafin hannunsa kan kunnenta"kafin tayi mgn ya murd'a kunnen....ihu da k'ara tasaki sbd azaba  har batason time din da ta'aza hannunta akan nasaba da nufin ta cire hannunsa.....wani mugun electrical shock sukaji atare da sauri AK yatureta ya janye hannunsa Yana Jan doguwar tsuka.....
Hhhhhhhhhhhhhhhh๐Ÿคฃ

     Da sauri AK yad'ago yaga waye ke dariya haka"suka had'a ido da Hafiz"tsaki abdallah yaja had'e da cewa k'ila kayi gamone ko?"dage gira hafis yyi had'e da cewa gsky nayi gamo nakuma alkhairi "gsky friend naji dadin ganunk....dallah yimun shiru Dan iska kawai....ke tashi kibawa mutane waje zannemeki ki karb'i hukuncin ki"haba Mana AK pls metayine?"Hafiz yakare maganar Yana kallon RIYAN daketa kuka sbd bakaramin murd'a Abdallah yyiwa kunnantaba"
       Tabe baki Abdallah yyi had'e da cewa laifi tamun"tashi riyan tayi batace komaiba tayi tafiyarta.
Hafiz kuwa cikin masifa yafara da cewa gsky baka yiwa RIYAN adalci"Wai Mike damun Kane Wai?katuna D'an Adam yanada daraja "sannan kada kayi saurin wulakantashi sbd bakason ko agaba ba zai maka Rana"kabi katakurawa yarinyar nan komai tayi laifine....look mlm dallah zakazo kanamun surutu aka,kokasan me tamun ne?

Sassauta murya Hafiz yyi had'e da cewa to Dan ALLAH friend kabari kaga yarinyace be kamataba irin wannan abin dakake Mata saita tsaneka wlh....so what ?"inta tsaneni "
To yanxun shikenan ni inasonta inkarabu da ita Zan aureta"tab'e baki Abdallah yyi had'e da cewa well in zaka iya.
Murmushi Hafiz yyi sbd dama yafad'i hakan ne dan yagane shin ko Abdallah ya Fara son RIYAN ne?"
Ahankali  Hafiz yace  Bata kyautaba gsky Amma Dan ALLAH kayi hakuri na rokeka dukda bansan laifintaba"tashi tsaye AK yyi had'e da cewa Ni fita zanyi in kagama surutunka muje"Hafiz bece komaiba sbd yalura abokinsa yyi nisa bayajin Kira.

   *******
Tun byn ta tashi ta koma d'akin ta,byn taci kukanta tayi  wanka tayi sallar la'asar"sannan taji zuciyarta tarage zafi"tunani tahauyi sbd ganin abban Abdallah datayi kamar ta tab'a ganinsa wani waje ko Kuma taga wani me kama dashi be"sai juye juye take wani gefen zuciyarta Kuma ta gudurci niyar in umma ta dawo dg k'auye zata tambayeta su wanene danginta,ma'ana dangin ummar sbd itadai dangin ubanta kawai tasani,ko adangin umma baffa sule yayan umma kawai tasani"inbata mantaba ta tab'a tambayar umma danginta sai ummar takama kuka.... Knocking d'in datajine yasakata dawowa tunaninta"tashi tayi taje ta bud'e"zulfa tagani tana Mata murmushi had'e da mik'a Mata kud'i tace Kinga Abdallah ya bani ayiwa ummana duk abinda ake bukata"murmushi riyanatu tayi had'e da cewa gsky natayi murna kin gode...zulfa tace dama hjy tace kije...Saida hantar cikinta ta kad'a Amma sai ta dake tace to gani nan zuwa , sannan zulfa ta fice...

Ajiyar zuciya riyan ta yi afili tace hmmm indai akan Abdallah ne ,dakin huta kirana,nida ayau zai sawakemun aura sa dayafimun sauk'i wlh ,sbd ta dauki alwashin zata guji duk wani Abu nasa dazaisa har yaga yamata mgn koya wulakantata.

Parlourn mom ta nufa ,byn ta yi sallama ta zauna a k'asa kan carpet.

Ayatsine mom tace abinda yasa nace akiraki shine jibi ake bikin bud'e campanin my son ,za'azo ayi Miki kwalliya sbd yadda za'aganki a waye baa bagidajiyarki ba .

Sannan munyi mgn da my son yace bbu laifi kinjin turanci Kuma mai miki lesson zai cigaba dg yau har ku rabu"

Sai ki iya takunki ,inhar naji kin gayawa wani ko wata AUREN WATA SHIDDA kukayi wlh ninasan abinda zanmiki Kuma agun taron kinuna ma duniya ku masoyane shima zanjamasa kunne kinajina?

Da sauri tace eh"

Wasu kayane cikin bak'ar leda ta mik'o Mata hade da cewa in angama Miki kwalliyar kibasu su shiryaki.

Kin gane?
"Eh hjy"
Ok Zaki iya tafiya"

Da sauri riyan ta dauki  kayan ta tafi d'akin y , sannan ta bud'e wardrobe tasaka ko ganinsu batayiba ,tana tambayar kanta wane campanine Abdallah zaibude?

Knocking taji,taje ta bud'e "zulfa ce tazo tace dama teacher d'in kine yazo"

Riyan tace to shikenan ganinan zuwa , sannan zulfa ta fice...


Da dare  byn tayi dinner"tana parlour jiran fitowarsa kod aakwai aikin da zata Masa ,sbd haka mom tace tarikayi kullum Kuma abincima yadda ake Bata da irin na y'an aiki ,yanxunma haka ake Bata irin nasu Kuma Bata damuwa.

K'amshin turarensa taji"hakan yasa tagane Yana parlourn"

Zama yyi kan kujera,beyi mgn ba itama hakan"

Can yace ke tashi kikamun coffee,"

Batace komaiba ta tashi taje ta had'omasa kamar yadda ya koya Mata"

Bayan ta aje Masa ta shi zata koma ciki"

Waya Baki izinin tafiya?"

Zama tayi had'e da cewa to mezanyi yanzun ?"

Ki kunnamun kallo"bbu musu ta tashi taje ta kuna tv da receiva"sannan ta ce saime Kuma?

Zoki dauki wannan ki ida shanyewa"

Kayi hakuri bantaba shaba,Kuma baya birgeni"

Kifara dg yau"

Dan ALLAH Ni bazan iya shaba Kuma Kingine"

What?kamar ya kingi?"ok nagane  nufinki kixo Kisha coffee d'in nan tun kina dariya ko Kisha atsiya.

Da sauri ta d'ago kanta suka had'a ido tsaki yaja had'e da cewa zakixo ki dauka ko kuwa?"

Hawaye ne masu zafi ke zuba a kumatunta gwanin ban tausayi"cikin kuka tace miyasa kakeson takurawa rayuwatane?"

Bansaniba"zakizo ko sainazo ? garama kiyi shiru Dan ko kukan jini zakiyi sai Kinshasa Dan bazan barsa ayi asaraba.

batace komaiba ta je ta d'auki cup din tashanye....tana yamutsa fuska tana kakarin amai.

Hmmm yarinya kika sake kikamun amai Zaki shanyesa"

Oya kima zauna "

Adole ta zauna kusan 20 minit,kafin tasaci kallon sa taga Yana kallon wani American firm"atashar mvc 2.

Zanje na kwanta Dan ALLAH!

Saida yagama Shan k'amshinsa tukum yace Zaki iya tafiya.

Da sauri ta shi har tana tuntube...

AK ya tab'e baki yacigaba da kallonsa....

Bayan kwana2

Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA ๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written
     By mmn fareesa


Wannan shafin nakune AUREN WATA SHIDDA FANS GRP2& MMN SHUKRA NOVELS.comments naku yafi nakowa yimun dad'i๐Ÿ˜ป
Love u guy's❤

  Not edited

P21

.....bayan kwana2
Zaune riyan take a bed room nata tana tunanin yaushe za'amata kwalliyar da mom tace amata"tunda talura yau Abdallah busy yake rabonta da shi tun safe daya fita har yanzun shiru"sai tunani take ALLAH yasa Yana lfy"
Wata zuciyar tace k'ila da gske yau ake bud'e campany din Abdallahn"

      Agogon d'akin ta kalla taga karfe 3:28 pm tashi tayi tayo alwarlal la'asar ta kabbar Sallah"
Byn ta idarne taji ana Knocking na kofar"tashi tayi ta bud'e Abdallah tagani tsaye sai faman Shan k'amshi take"da sauri tace kadawone?"tun safe daka fita baka dawoba lfy dai ko?"tab'e baki yyi had'e da cewa me ruwanki da dawowata da rashin dawowatane?"
Kizo wanka zanyi tunda ke Baki gadamar shiryawa ba Kuma karfe 5:0pm za'a yi taron.ni bazan tsaya jirankiba....Baki bud'e riyan ke sauraren wad'annan bak'ak'en maganganu da Abdallah ke yab'a mata har yakai aya ya juya yyi tafiyarsa...

""Bed room nasa tabisa tasamesa Yana rage kayan jikinsa"kauda kanta tayi had'e da shigewa toilet d'in ta had'a Masa ruwan wanka kafin ta fito"dg shi sai boxer da towel a hannunsa Yana jiran ta fito ya shiga"
Atsorace ta rufe idonta sbd ganin yadda yake, ga uban gashi kwance afaffad'an kirjinsa"
    Jikinsa a murd'e duk gashi"tsaki yaja had'e da cewa Zaki bud'e idon ko kuwa?
Dan ALLAH kayi hakuri bazan iyaba wlh niba y'ar iska bace"lallai yarinyar nan kingama ganin gadon baccina wlh ok kifito kawai kice Abdallah Dan iska kawai...wlh wlh niba haka nake nufi ba kawai d....rufemin baki,ki tsaya kishiryani Inna fito sannan kije mom zata saka amiki kwalliya, sannan kima kamaa kanki agurin "kikamun hauka ko kanyanci wlh muka dawo tare d karnukan gdn nan Zaki kwana.. mittsss yaja tsaki hade da shigewa toilet d'in.

Zama tayi gwanin ban tausayi sbd tana mugun tsoron kare ne ,sbd jiya yaga sadda tashigo da gudu Kuma atsorace yace lfy ,tace karnuka suka biyota shine zaice intamasa laifi acikinsu zata kwana..,,,,

Befi 15 minit ba yafito sbd Yana sauri inyashirya zaije Gurin Abba ,insannan anshirya riyan su wuce"

Kanta na duk'e yace ke duba wardrobe dg sama kayana nan ki mik'o min , yafad'a Yana kokarin shafa mai"
Tashi tayi taje ta dakko ta aje gefen bed,kafin tace saime ?"kifito mun da agogo da takalmi"
Ahankali tace a Ina?"d'agowa yyi yaja tsaki hade da cewa ok bakisaniba?"Inna sani mezaisa na tambaya"nikike gayawa mag... afusace aka murd'o kofar"atare Abdallah da riyan suka d'ago Dan son ganin waye"mom ce ta shigo kamar anjehota" afusace tace bakada hankali Abdallah ?" Dubeka a have nerket Amma kake tare da munufukar yarinyar nan,tayimaka uwarme ?"
Cike da mamakin ta Abdallah yace haba mom me kike zargine? Kinsan koni waye inma bacin kun likamun ita bazan iya tsayawa ba har nakirata  tamun wani Abu,,Kuma ko yanxun kayana ne zata fitomun dashi... mittsss kayan banza ,Zaki fita kije dakinki masu make up najiranki ko kuwa?"suna can natura su ,sundawo sunce Baki can Ashe kina nan munafuka....riyan da kanta ke duk'e tayi saurin ficewa dg d'akin, yyinda mom ta dubi Abdallah had'e da cewa dg yau kada nakoma ganin yarinyar nan acikin d'akin nan"kaji koba kajiba?"
Fuska bbu walwala yace naji....fuuuu tafice tamkar wata kububuwa..lolx.,,,,,,,,

    Bangaren riyan kuwa tanashiga ,aka hauyimata make up sbd dama da wankan ta"sai yaba kyan ta suke har suka gama Mata kwalliyar ta fito musu da kayan da zata saka"
Sai asannan taga doguwar riga ce gwont dark blue sai Yar ciki Fara sai veil dark blue da takalmi dark blue....
Hmm..zanso me karatu yaga irin kyawun da riyan tayi,ga k'amshi na musammun dake fita ajikinta,byn sunmata rolling ta dubi kanta a mudubi....zaro ido tayi tana dubar kanta... murmushi masu kwalliyar sukayi had'e da cewa Masha ALLAH Kinga yadda kikayi k'ila ma mai gdn yakasa ganeki"

Kafin tayi mgn zulfa ta shigo had'e da cewa amarya kije inji angon"tafad'a cikeda zolaya"

Murmushi riyan tayi had'e da cewa to gani nan"sannan tayi sallama damasu kwalliyar suka fita.

Sake kallon kanta tayi a mirro,tayi tasbihi ga ALLAH dakuma godemasa da irin baiwar halitta dayayi Mata"

Ahankali ta canza lafiya tana wani yatsina d amotsa Baki ,tana dubar kanta a cikin mirro,taga intayi hakan Abdallah bazaice tayi wani kauyanciba sbd ita ayanxun ganin kanta take daidai da kowace mace,fatanta ALLAH yasa zeenat taje Gurin saitayi abinda tasakata zubda hawaye.

Jin ana knock yasa tayi saurin daukan post nata ta fice.

Ahankali take tafiya har ta iso waiting parlour inda Abdallah yakeda zugar abokansa"wadanda sukayiwa riyan k'uri da ido "yyinda gogan be kalli inda takeba dukda yanajin sautin Karan takalminta,hankalinsa nagun waya"
Masha ALLAH Hafiz ke cewa a zuciyarsa sbd da ace banan yagantaba to wlh bazai ganetaba inba muryarta yajiba.
Da k'afa ya zunguri Abdallah dashima yyi masifar kyau cikin dark blue na suit da takalmi da agogo duk dark blue ,sumarsa Tasha gyara sai salk'i take...
Cikin kak'aro murmushi yad'ago sbd bayason friend nasa su fahimci wani Abu,in ancire amininsa Hafiz"Dan sake ware ido yyi sbd ganin wata shuwa Arab din yarinya,yyi saurin dubar Hafiz,shikuwa yad'aga Masa gira"alamar eh itace"cike da basarwa yamike tsaye Yana wani shu'umin murmushi... adedenan cpt suleiman yace wow AK ka iya zabe' ammafa batafi iftihal d'ina ba komai(INA TARE DA ITA ) kallonsa AK yyi had'e da cewa dubadai"sannan ya dubi riyan data ida isowa"cikin murmushi yace gsky baby kin shanyamu da yawa"cikin dakiya riyan ta shagwab'e fuska tace to bana ce muje basai ammun make up d'in ba kace sai anyi....hmmm kincika rigima wlh ai in ammiki zakifi kyau ko?"yafad'a Yana murmushi had'e da mik'a Mata hannunsa"yace ga friends nawa ku ki gaidasu,cike da tsoro ta aza hannunta kan nasa, sannan tace hii!sannunku da zuwa!gsky Ina fushi daku tunda sai yau kuka tab'a visiting namu"
Baki bud'e Hafiz ke kallon wannan dirama ta riyan da Abdallah sbd tayi bala'in basa mamaki riyan.

Duk murmushi sukayi ,kafin Hafiz yace laifin mijinkine dabe gaiyaci wasuba a bikin naku saidai sukaji labari yyi aure...

Harararsa Abdallah yyi had'e da cewa "laifinka daiko"muje kada muyi latti"shagwab'e fuska riyan tayi had'e da cewa nidai gsky da nisa kafin mu isa get kadaukeni..... hhhhhhhhhhhhhhhhhhh๐Ÿคฃ๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜„๐Ÿ˜ป  duk suka saka dariya" sir Aliyu (nida d'alibata) yace gsky AK kuna lokaci kaida madam, wannan irin shagwaba da kayi Mata...cikin dariyar yak'e Abdallah yace to badole na shagwabata ba"yafad'a Yana muntsinin Riyan....da k'yar da daure batayi ihuba.

Ahankali Hafiz yace to ai tunda kashagwabata ko kunyarmu bakwayi saika dauketa ko"kallon gargadi Abdallah yyi Hafiz da riyan,saima Hafiz yyi tamkar bejiba.

Mlm riyan kuwa sai ta turje ita adole sai ya dauketa,yyinda hafis keta danne dariyarsa sbd yasan mutumin ya k'ulu"

Janyota yyi jikinsa suna kokarin ida fita dg cikin parlourn....wani yarrrrrrrrrrrr!yaji ajikinsa Amma sai yadaure,yakai bakinsa daidai saitin kunnenta"wata irin kasala riyan taji ajikinta"cikin masifa yace ke wlh ko yi tafiya da kanki ko ki kwana yau Gurin karnuka nizaki saka nayi dakon wannan k'azamin jikin naki.

Ita kuwa shiru tayi sbd ta k'udurta aranta saifa ya dauketa kodan zeenat da mom suji haushi sbd tasan suna a compound din gdn jiran fitowarsa.

Saurin janye jikinta tayi dg nasa tace shikenan nibazan jeba"Hafiz dake bynsu yace haba AK miye aciki?

Duk yadda kke sonta sbd ganin mu kak'i daukanta"

Abdallah jiyake kamar yarufe Hafiz da suka Amma bbu hali.

Yarima Ashman datun d'azun beyi mgn ba sbd kasaita "ahankali yace towai miyasa baza ka dauketa ?immune munyi gaba a mota mujiraku sai muwuce ko"

Hafiz yace hakane ai zai dauketa ma sbd aishi yashagwaba ta"

Cikin bak'in ciki Abdallah ya Suri riyan Yana murmushin yake,yyinda ita Kuma ta aza hannuwanta ta zagaye wuyansa dasu,tana murmushi.... adedenan Hafiz yyita musu pics .

Abdallah yyi mamakin jinta sakwab,azatonshi zatayi nauyi,sai hararan Hafiz yake yana Masa alama da ido yabari"

Amma yaki bari,shikuwa Abdallah shikadai yasan hukuncin dazai yankewa riyan .

Haka yasabeta har suka iso campaund din gdn....atare mom d zeenat suka tashi tsaye...

Da sauri mom ta nufi gurunsu.

Tun dg nesa....

Share pls

BY
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



Story & written by mmn
    Fareesa


Dedicate to all my fans๐Ÿฅฐ๐Ÿ˜˜

Kuyi hakuri narashin posting d'ina inada uzurirrikane ,masu kirana dan jin lfy ta nagode sosai wad'an da banma reply ba a what's app pls kuyi hakuri"banida time nagode sosai...



   p 22

""Tun dg nesa riyan ta hango su mom sunmike tsaye itada zeenat kowacce fuska da mamaki... duk'ar da Kai tayi ,tana dariya kafin ta d'ago taga mom gab dasu fuskarta daure,yyinda friends nasu AK ke kallonta"
Tana isowa tace kai
     Abdallah meye haka nake gan....kallon da Abdallah yyi Mata da ido had'e da nuna Mata abokansa yasata yin shiru,ta k'akaro murmushn takaici d bak'in ciki"
Ita kuwa riyan Yana sauketa ta juya bayanta ta Dena kallon mom tana sauraronta taji dame tazo?"sai taji tayi shiru"
Mom kuwa dubar riyan data juya baya take , azuciyarta kamarta rufeta da duka ,ta daure tace y'ata yayadai kin juya baya?" Kushiga mota Mana"


 
      Murmushi riyan tayi had'e da juyowa tace ok mom sai mundawo "ta fad'a had'e da dagawa mom hannu "sannan ta fakaici idon kowa ta yiwa zeenat gwalo wadda  dg nesa tana kallonsu..
Hannunta Abdallah yakama yabude wata mota me kyau yasakata,kafin yashige sauron abokansa surufa Masu baya"
    Mom ta bisu da kallo har suka b'acewa ganinta"ahankali tace hmmmm ALLAH yasa ayi taron lfy kafin komai yazo karshe kilama bazaki Kai WATA SHIDDA ba zansaka yasakeki....ah ah kada kiyi haka kawata ai plain namu bazai tafi daidaiba kibarta kawai cewar hjy ikilima  tana dafa kafad'ar mom, yyinda zeenat ke kusada da ita tana hawaye...


Inmukayi hakan tana gdn bbu komai kuwa?" Cewar mom tana kallon hjy ikilima.

Yo eh Mana"

Bara kiji kawo kunnenki"nan ta rad'awa mom wata mgn suka shek'e da dariya.

Kafin mom ta dubi zeenat da mamaki tace lfy dai ko kike,Kuma miyasa bakije gun taron ba??"

Hmmm hjy hafsat rabu da marrar tunani wahalallar banza,ita a haukanta kishi take shiyasa take kuka ko"dubarta mom tayi had'e da kashewa hjy ikilima ido tace sorry kinji y'ata kidai Bari yarabu da ita dolensa ma ya aureki... murmushi zeenat tayi had'e da cewa yauwa mom  amma Dan ALLAH kada kuyiwa abdl....ke rufemin baki wuce muje....shiru zeenat tayi had'e da bin byn hjy ikilima dkewa mom sallama.,,,,,


    Bangaren Abdallah da riyan kuwa, byn sun shiga mota riyan ta matsa tayi nesa dashi" Abdallah kuwa yaso yyi Mata rashin m amma ganin driver najinsu sai ya k'yaleta kawai Yana murmushin yake had'e da  matsawa gab da ita yakama hannunta ya matse cikin nasa gam Yana Mata mugunta...ita kuwa daurewa kawai take tamkar tasaki ihu sbd azaba"
Matsowa yyi da kansa   kusada fuskarta"cikin sweet voice insa yace hii baby! akwai zafi?" ko nakara ?" banza tayi dashi tama rufe ido"murya k'asa k'asa yace zanbaki mamaki yarinya sbd kin sakani yin dakon wannan k'azamin jikin naki ....niwai Zaki ce nayi dakonki ko?"sbd gaki jarababbiya kina son had'a jiki Dani to kibari innarabu dake saiki auri jarababbe D"an uwanki kutaru kuyita jarabarku" "hmmm inhar mukashiga Gurin nan kikamun iyayi wlh muka koma gd Zaki gane bakida wayo....saurin janye fuskarsa yyi sbd ganin anyi parking....

Driver nayin  parking yafice dg motar"

AK Yadubi riyan da idanunta ke rufe"

Yace keeeeeeeeeee!

Bud'e idanunta dasukayi jajir tayi ,sbd bak'in cikin kalaman da Abdallah yagaya Mata San ranshi..

Batace komaiba ba tana sauraronsa"

Cikin ko inkula da yanayinta yace abinda zan fad'a Miki"shine kikama kanki kada kisake kimana hausa ko body language,kinji ko bakijiba?" 

To "ta fad'a atakaice"

Fitowa yyi ganin anbude Masa motar"Hafiz ne ke murmushi Yana cewa haba abokina wannan soyewa haka ,kamar ba gida d'aya zaku kwanaba "ai yakamata kufito hakan!yo wannan kana ma iya zuwa office kuwa?"sbd soyayya,ainas...mugun kallon da Abdallah yyi masane had'e da take Masa k'afa yasashi yin shiru Yana dariyar tsokana....saidai fa dariyar tasa ta tsaya sbd ganin fuskar riyan wata iri ba kamar d'azunba.... azuciyarsa yace AK ne kuwa yayimata wani Abu"
     Hannun riyan yakama had'e da rungumota tuni camera ta Fara haskasu ,kowa na Gurin cewa yake Masha ALLAH sbd ganin couples d'in "ita kuwa riyan binsa take suna tafiya cikin nutsuwa Amma ranta fal bak'in ciki ta dau alwashin duk radda yasake yanemi wata alfarma gunsa zata basa mamaki...


     Tuni MC yafara bayanin abinda yatarasu anan sbd ganin AK da riyan sun zauna ga abokansa abayansa" yyinda Abba da manyan mutane ke zaune gefe da sauran jamaa ,byn annatsu aka Kira AK yazo sbd ya yanka farin k'yalle"tashi yyi tsaye had'e da mik'awa riyan hannunsa ta kama ta tashi ,saita noke kafad'a alamar shagwaba.... azuciyarsa yace nafi iyawa"rank'wafowa yyi da kansa yace inhar kikbari nabar nan Baki biniba zanbaki mamaki"murmushi tasaki had'e da kama hannunsa ta tashi tsaye....tafi da sowa mutane suketayi sbd kowa azatonsa suna son juna ne,yyinda Abba keta murmushi sbd yazata ko Abdallah yafara son matarsa ganin yaduk'a azatonsa rarrashinta yake...

Ahankali riyan ta aza hannun ta kan na Abdallah byn sun isa Gurin ,nan ya yanka aka hau tafi sannan aka hau ciye ciye da Shan abin sha ,gefe guda kuwa music ketashi,riyan kuwa bataci komaiba ba" saidai Abdallah yasha drink kawai"byn duk su Abba sun fice akayita matsowa kusada su ana musu ALLAH yasa alkhairi !Koda riyan ta lura da mutane sunyi yawa saita sulale ta fito ta nufi Gurin motar dasuka zo" da sauri wani guard yabude Mata tashiga"saidai hafis duk Yana lura da ita da sauri yabiyota yaga Ina zata tafi" Koda yaga tashiga mota ,gun motar yanufa...turus yayi sbd ganin tana kuka harda shashsheka....da sauri yace riyan lfy kuwa?miye abdallah yyimki kike kuka haka?"

Yakusa minti5 tsaye Yana Shirin tafiya ma sbd ganin Taki kulasa...yaji tace yah Hafiz meyasa Abdallah besan darajan d'an adam ba?

Ajiyar zuciya Hafiz yyi had'e da cewa Mike faruwa ne Dan ALLAH?

Cikin kuka tasanar da shi kalaman da Abdallah yaga yamata"ta kare da fad'ar to Mike nufinsa?ko yaan zargina ne kome?"

Ya isa Dan ALLAH riyan'kiyi hkri kibarwa ALLAH bkinji sannan kada kikoma nuna Masa ranki na b'aci inyayimiki Abu ,kinuna ko inkula insha ALLAH zai bari Kuma Dan kicigaba da addua had'e da hakuri ni inaji ajikina akwai wani babban al'amari dazaifaru gaba kad'an riyan kinji....

Shiru tayi tana nazarinsa"ajiyar zuciya tayi had'e da cewa nagode sosai yah Hafiz"

"Murmushi Hafiz yyi yace ba komai ki goge hawayenki ki nutsu kada yagane kinyi kuka kinji bara na koma gurinsu sbd Kinga anata fitowa da alama antashi....


Abdallah kuwa be lura da tashintaba "sai gaisawa d  jama'a yake harsuka rage kafin yalura Bata nan"

Tab'e baki yyi alamar ko ajikinsa ,tashi yyi ma Yana neman Hafiz be gansaba, sallama yadunga yi mutane yyinda yaketa yan waige waige ko yaga riyan Amma be gantaba Kuma gashi bega hafis shimaba,tsaki yaja had'e da cewa ita tasani matsalar ta"

Fitowa yyi su CPT SULEIMAN da SIR ALIYU abayansa suna cewa Wai AK Ina sahibar takane?"tabarka Kai kadai...cikin kak'aro karya yace eh tana mota "waya take sbd ciki bbu network... yafad'a yanajin haushin yau yyi k'arya sbd wata can bacin yatsani yin k'arya ko mak'aryaci arayuwarsa... adedenan Hafiz ya iso gunsu Yana cewa AK ga riyan canfa amota tana jiranka...

Ajiyar zuciya yyi sbd jin maganar Hafiz tazo daidai da karyarsa.

Bece komaiba ya yimusu godiya had'e da sallama kowa yashige motarsa...


Bud'e masa mota akayi yashiga cikin isa had'e da kasaita, yyinda riyan ko inda yake Bata kallaba,shima haka sai latsa wayarsa yyita yi har suka iso gd..

Ana gama parking riyan ta bud'e kofar kusada da ita ta fito ,tanajin Abdallah nacewa ke jirani...tayi Masa banxa.

Afusace yafito ,Amma tayi Masa nisa,kamar ance ta juyo taga yabiyo bynta sbd azatonta part d'in mom zai nufa.

Da sauri ta nufi part d'in su,tayi saurin shigewa bed room d'in ta ta saka key,ta jingina da kofar tana 
Sakin ajiyar zuciya....

Bam !bam!!bam!!!

Abdallah kedukan kofar kamar zai balle kofar...

Riyannnnnnnn!

Nace ki bud'e kofar nan ko"

Inkika bari na kirga ukku Baki budeba wlh saikin sani kinji na rantse.....

One!twoo!!!thre.....


Share 

BY MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by
   mmn fareesa


  p23

One !two!!three!!!kafin yarufe bakinsa ta bud'e kofar tana kallonsa Bata ce komai ba"afusace yace gsky kin ceci kanki Dan wlh dabaki bud'e ba nidake ne agdn nan"oya kije kiyi magrib "inkin idar kije bed room d'ina kayan wanki na nan adaure ki wankesu,hukuncin sani dakon k'azamin jikin ki..... murmushi tayi had'e da cewa to shikenan"tafad'a tamkar bataji haushin sakata wankinba"
   Cike da mamaki take dubanta harta juya ta koma cikin d'akin"tab'e baki yyi had'e da nufar bed room nasa yyo arwalal magrib yanufi masjeed"
   Bedawoba ba sai byn isha'i yawuce part d'in mom"
Zaune take tana kallon TV, murmushi tayi had'e da amsa sallamar sa"byn sun gaisa ta Masa fatan alkhairi kafin ta gabatar Masa da abinci"
Byn yagama dinner d'in suna fira da mom Abba yashigo rik'e da jarida a hannunsa ya zauna gefen mom suka cigaba da fira da shi har kusan 9:35pm kafin AK yyi musu sallama yafito, yanaso ya kwanta da wuri sbd gobe karfe 8:am zaifita office"

    B'angaren riyan kuwa byn ta idar da sallar ta je ta duba tulin kayan wankin sunkai set 16 ,danba basuda datti"wani kunci taji da bak'in ciki aranta amma data tuna INNAL LAHA MA'ASSABIRIN da Kuma INNA MA'AL USRU ISRAH...sai taji zuciyarta tarage zafi"wani tunani tayi da sauri ta koma gefen dayake motsa jikinsa ta dakko washing machine ta saka kayan ya wanke su tas Bata sha wahala ba"duk da atsorace take gudun kada yazo yatarar,Bata idarba sai 8:52 pm ta nufi Gurin hanger ta shanyasu byn ta maida washing machine d'in gunda ta d'auka.
Bed room nata ta koma ta yi isha'i had'e da sha'fa'i da wuturi "taci abinci ta kwanta cike da kewar ummanta...

Abdallah kuwa be shiga bed room nasa ba Saida yaje yaduba yaga ta wanke kayan tukum...saikuma yaji tausayinta,wata zuciyar tace yanzun in y'arka ce aka yima haka zakaji dad'i?"
Shiru yyi Yana tunanin tunda riyan ta zo gdn yake mata rashin kyautatawa,sai yaga be kyautaba duk da wani Time din ita keja ana Mata hakan.amma insha ALLAH zai Dena takurata har lokaci yyi yarabu da ita ya huta, kafin yyi ajiyar zuciya ya koma bed room nasa "ya wuce toilet ,da kansa yahad'a ruwan wanka kafin yyi...
Bayn ya fito yashirya ya kwanta....

  ********
Washe gari tunda wuri riyan ta tashi taje ta gyare masa ko Ina ta had'a Masa ruwan wanka kafin ta fito dg toilet d'in"ta dubi agogon dake jikin bango taga 7:14 am "afili tace anya ba8:am bane zai fita office?"
Nufar gadon tayi ta dubesa Yana kwance atsakkiyar gadon ya rufe jikinsa da bilencat,fuskarsa ce kawai ake gani"k'uri da ido tayimasa azuciyarta tace Masha ALLAH mutumin nan badai kyauba"matsalar sa girman Kai... ahankali ta Kai hannunta kan pillow tad'an bubbuga tana cewa katashi kada ka makara"
   Yakai kusan 2 minit kafin yasoma motsa golden eyes nasa,harya waresu akan agogan bangon d'akin"tsaki yaja had'e da dubar riyan wacce kanta ke duk'e tanajiran yafara Mata masifa"shine Dan wulakanci sai yanzun Zaki tayar Dani?"yaushe harnayi wanka na gaidasu mom har natafi office?"

Bata dubesa ba tace kayi hakuri ,yanzun ma nayi kasadar tadakaine Amma kaje kayi wanka lokaci na tafiya"harara ya gallamata dukda ba ta kallon sa,jin motsin zai tashi yasata saurin juyawa da nufin fita"oh bazama kijira kitayani shiryawa ba ko?"shine Zaki give"baat juyoba ta tsaya sbd batason ganinsa help nercat"suit Zaki fito mun dasu "to saika fito"banza yyi Mata yadauki towel yashige bathroom d'in....
Ajiyar zuciya tayi had'e da nufar wardrobe ta fito Masa da suit red ta feshe su day design na performance nasa,ta curo Masa takalmi da agogo bak'a k'e ta duk'a tana goge takalmin sbd gudn masifarsa duk basuda k'ura to tasan shi mai tsabtane sosai... adedenan yafito daga toilet d'in"sai yaji ta kyauta sbd yanason tsabta"fuska bbu yabo bbu fallasa ya ce fitomun da brief case d'ina!to tace byn ta aje takalmin gefen mirro, yyinda yacigaba da sha mansa,harta kawo Masa"had'e da laptop nasa"ahankali tace gashi...tsaki yaja had'e da cewa Wai miyasa bazaki iya kiran sunana ba ne?"saikace Baki saniba "karki Bari nakoma Miki mgn"kayi hakuri bara najiraka aparlou kasaka  kayan !Bata jira amsarsaba ta fice dg bed room d'in..

  Cire towel din yyi, sannan ya ida shafe jikinsa yadauki kayan cike da mamaki yadubesu jin suna k'amshi wato ita tasaka turaren kenan"afili yace bbu laifi ta fara wayewa! Kafin yasaka kayan agaggauce yagyara sumarsa yafito da agogo ahanunsa"tana ganinsa ta shi vta karb'i agogon ta d'aura masa Yana duba wayarsa harta idar,kallonta yyi up& down yaga doguwar riga ce fited gownt maroon ajikinta,da wata huta baka tayi acuci...dagowa tayi suka had'a ido...saurin kauda kansa yyi cikeda basarwa, ahankali tace amma ko tea ne zakasha ko?

Ah ah bazanyi break ba gsky"

Amma katafi baka karyaba"

Laifin wa?"

Shiru tayi had'e da dukar da kai k'asa...as from today kada kikoma sakamun acuci maza acikin gd,ko kin dauka bansanshiba ne? Axotonki kija ra'ayina kome....indai acucine to duba na cire,ta fad'a had'e da cire hular kanta...tuni bak'in gaahinta mai tsawo da salk'i yabaiyana"kallo d'aya AK yamata yadauke kansa sbd ganin tabbasa gashintane tayi acuci dashi'yyi mamakin yawan gaahinta Amma be nuna ba.

Ita kuwa hularta ta mayar,tana cewa bara ko tea d'in ne nahada maka kasha .

Bata jira amsarsa ta wuce dinning area and had'a Masa ,ta dauko ta aje gabansa , yyinda shikuma yake waya da Hafiz.

Bbu musu yadan sha kusan fin rabi ,ya aje cup din had'e da cewa muje kiraka Ni....um um amma kamance hukuncin mom na tahanani binka ko Ina?ok banida suna ko?ah ah Yaya Abdallah.... murmushi yyi mai sauti yace ok haka Kuma nasamu y'ar kalan dangi,dukda banida kani ko kanwa ,aibance Ina nema ba ko"hmmm inma kayi wannan tunanin baka canka daidiba Inka tuna ma abokinka  ma Yaya Hafiz nake kiransa sbd bana iya Kiran sunan Wanda ya girmeni Kai tsaye....am...is ok muje aininace ko"
    Babu musu ta bisa, brief case d'insa na a hannunta ,ahr suka iso gabda part d'in mom....dakatar da ita yyi had'e da cewa jirani anan...
Ajiyar zuciya tayi sbd hakan yafi Mata sauk'i da masifar mom.


   Bejimaba yafito,tabi bayansa gab dazasu isa get ya karb'i kayansa had'e da cewa Zaki iya komawa ciki...ok adawo lfy ALLAH yabada saa,akan  labb'ansa yace ameen,kafin yanufi Gurin body guards nasa dake jiransa....

Masha ALLAH Abdallah yaje office yafara aiki lfy duk da yamaka, acan Kuma Hafiz da feedo suka samesa suka sakemasa fatan alkhairi,"anan Hafiz kw rad'awa AK akunne cewa my man munkusa Zama fa iyaye muma sbd nacika aiki madam laulayi take... yafad'a Yana dariya had'e da dagowa yace saura Kai ma yaka....shiru Hafiz yyi ganin mutumin ya had'e rai yasakashi jin shiru yyinda feedo ke murmushi tana kallonsu sbd bataji me Hafiz yaradawa AK ba.


    ########

Kwanci tashi bbu wuya Gurin ubangiji yaudai kimanin sati   6 kenan dafara zuwan AK office,Masha ALLAH yanata ganin ci gaba yyi suna ta fannin iya Zane da kwarewa sai kwangila ake kamasa ta gine gine ya zana ,yasaka agina abun sai godiya,tuni yakara yin suna a kd harda wajenta, arziki yakara bunkasa saidai har yanxun miskilancinsa na nan ,gwfe guda na zuciyar sa yanajin zafin abinda mom keyiwa dad , sannan yatsani hjy ikilima sbd yasan ita ke aza mom akan duk wani abin k'ii...
Gefe guda Kuma watansu 2 kenan da riyan, ak'agare yake 4 month yacika ya sallameta,duk har yanxun be Dena yimata abinda yakeba saidai yarage kaso ukku acikin  goma na abinda yake Mata...

Zaune take kan kujera tana tunanin ummanta har yanxun tak'i dawowa tana k'auye gashi aun Dena waya ,Amma bara mutumin nata yadawo k'ila intasamu Yana cikin Yan arzikin yabata wayarsa takira umman.... k'amshin turarensa dataji yadaki hancinta yasa tagane yashigo parlourn.

Kallonsa ta sata tga fuskarsa bbu walwala kamar Kuma yanada damuwa"

Ahankali tace sannu d xuwa"

Yauwa"yafad'a atakaice.

Karbar brief case nasa tayi had'e da daukar takalmin daya cire ta nufi bed room nasa.

Btafi 5 minit ba ta fito tana cewa Yaya Abdallah kaje kayi wankan....
Riyan abar wankan nan bazanyiba.

Da mamaki take dubarsa,sbd jin Wai abar wankan nan"mutumin da saiyyi wanka sau 4ko5 arana ma, ahankali tace kayi hakuri kaje kayi tunda kadauko gajiya a office kaji dad'in jikinka ma.

Banza yyi Mata,sbd yau kwata kwata bayajin dadin jikinsa,ga faduwar gaba dayaketaji tun dg jiya da dare har yau besan dalilin jintaba.

Amm kayi hakuri Inna maka shishshigi Naga tun jiya kamar kana cikin damuwa ko?

Nima bansaniba , sannan pls kirabu Dani "

Bejira asartaba ya nufi bed room d'in sa,badan yasoba yyi wankan da alwarlal magrib yafice zuwa masjid.

Bedawoba sai byn isha'i,Kuma yashige bed room nasa be nemi kowaba ,beci dinner d'in da aka jaemasa a dining table.

Ita kuwa riyan k'yaleshi tayi kamar bukata"9:pm nayi tayi kwanciyarta.

Washe gari byn riyan tayi sallar asuba ta koma ta kwanta sbd ganin week end ne bbu office dukda zataje islamiyar safe sbd Bata Dena zuwaba.

Bata jima da kwanciya ta farka agigice sbd mummunan mafarkin datayi taga Abdallah acikin baccinta.

Da gudu ta nufi bed room nasa ,bbu ko sallama ta kutsa Kai ciki..

Kwance tasamesa kamar.....


Yanzun aka soma labarin sbd abaya baa Fara komaiba,bana bukatar steakers ko godiya comments kawai ko kuji shiru...


BY 
MMN FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบAUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ



  Story & written by
mmn fareesa

Wannan shafin sadaukarwane ga masoya wannan novel aduk inda kuke Naga comments bbu adadi had'e da fatan alkhairi agareni,naji dad'i . sannan kuyi hakuri da rashin post akai akai inada uzuri wlh...๐Ÿฅฐ๐Ÿ˜˜



Not edited

  p 24
..... kwance tasamesa kamar matacce! Inbacin idonsa da ke motsi data d'auka cewa ya mutune"
Sbd ko motsi bataga yanayi ba "ahanzarce , Had'e da kid'ima ta nufi gefen gadon tana cewa Yaya Abdallah!Yaya Abdallah!!yaya Abdallah!!!Amma shiru Kuma Yana kallonta.
Inna lillahi wa inna ilaihir Raju un kawai take maimaita wa had'e da Kama hannunsa Amma saitaji hannun asake kamar matacce"zaro ido tayi ta girgiza sa"tana cewa kayi mgn Dan ALLAH!
Hawaye tagani na zuba ta gefen idonsa hakan ya tabbatar mata yanada Rai" wani mummun abune ke Shirin samunsa koma yasamesa"runtse idanunta tayi sbd tuna mafarkinta nad'azun!da sauri ta saki hannunsa ta fice dg bed room d'in cikin tsantsar tashin hankali....
Yyinda Abdallah yyi zugudum akwance sbd ko hannunsa baya iya d'agawa balle Kuma yyi mgn "azatonsa ma ko mutuwa zaiyi,gashi yanajin maganar riyan Amma baya iya mgn shi,ko tashi balle har ya iya tafiya"abinda kawai yake iya amfani dashi ajikinsa....IDO..tun bayan sallar asuba ya kwanta bacci yyi wani mafarki da wata dattijuwar mace kyakykyawa tana kiransa Yana kok'arin zuwa Amma ta Masa nisa ga Daddy nason yaje gunta ga mom najan hannunsa ta hanasa zuwa da k'yar ya fisge hannunsa dg na mom zai tafi Gurin matar sai yaga Rami gabansa zai abka sai riyan tayi saurin rik'e sa... adedenan ya farka !Amma me ?sai yajisa cikin bak'on yanayin dabaitab'a riskarsaba arayuwarsa.
    Yyi yayi yatashi ta kasa Koda motsa hannunsa balle bakinsa dayyi tamkar anrufe masashi   "ambaton ALLAH kawai yake ana cikin hakan riyan ta fad'o dakin"to Wai meke Shirin faruwane Dani?"yafad'a azuciyarsa....

     Riyan cikin tashin hankali ta kutsa Kai parlourn Abba "bbu ko sallama"akidime ta dubi Abba dake dining area  tsaye Yana Shirin hadawa mom tea , yyinda mom ke zaune busa kujera 1 dake gaban dining table d'in"Abba! Abdallah..ne  ..ne bashi...bashi... mitttsss dallah inzakiyi mgn kiyi inbazakiyiba ki fice kibawa mutane guri"cewar mom tana watsowa riyan muguwar harara"
Yyinda Abba gabansa yyi mummunan faduwa "da sauri yace lfy dai ko?meyasami Abdallan??"
Cikin kidi'ma tashiga sanar dasu...LA'ILAHA ILLA ANTASSUBA NAKA INNI KUNTI MINAL ZALIMINA!WALAHAULA WALAQUWATA ILLA BILLAH... abinda Abba keta maimaitawa, yyinda mom ta kurma uban ihu had'e da cewa nashiga ukku ni hafsatu"meya ke Shirin samunka Abdallah?"
Shiru riyan tayi tana dubansu kawai,kafin Abba cikin tashin hankali Yadubi mom yace muje mugansa...


Yadda tabarsa ,haka suka samesa!da gudu mom ta nufesa tana kuka da surutai tana girgiza sa da Kiran sunansa cikin zubda hawaye, yyinda Abba ketsaye  gaban gadon yana kallonsa cikin tausayi da son D'an nasa tilo guda aduniya, idanunsa sunyi jajir "gefe guda Kuma riyan itama hawaye take sbd tausayin Abdallah,takuma k'ara Imani da ALLAH meyin yadda yaso alokacin dayaso "jiya iwar haka take fito Masa da kayansa har Yana cewa ta canza,Amma yanzun dubesa shida matacce banbanci kad'an me, lallai mutum ba'akin komai yakeba agurin ubangiji zaibaka lfy da rashinta  assada yaso.... maganar Abba ce ta katse Mata tunani,daya ce bara na Kira ya'u direba da Hafiz abokinsa mukaisa asibiti "
   Gimtse fuska mom tayi had'e da sakin Abdallah dake jikin ta ,ta maidasa  kwance tace ah ah Alh basai anwani Kira Hafiz ba akiradai ya'u direba d'in"
Ok" yafad'a atakaice kafin ya fice da hanzarinsa...
Kallon Abdallah mom tayi taga yarufe ido,jikinsa ta duba taga jallabiya ce Fara yasaka,da alama da ita yyi sallar asuba kenan..
Cikin kuka tace Abdallah kana mgn ko baka iyawane?Kuma kanajina be?"
Cikin mamaki riyan ke sauraren wad'annan tambayoyi na mom dasuke da alamar ayi Mata itama tambaya"
Abin mamaki sai Abdallah be bud'e idonba koya  motsa bakinsa"hakan yasa tasaki kuka tana cewa wayyo ALLAH yanxun ko ji da mgn bakayi Abdallah"
Oh ALLAH yabaaka lfy!

Kallonta ta maida akan riyan dake hawaye"cikin hantara da tab'e baki tace to ke asuwa kike kuka?"

Girgiza Kai riyan tayi,sbd yau taji kwata kwata yau bbu tsoron mom atare da ita.

Kai tsaye tace ,Ina kuka sbd Ina tausayinsane dakuma tausayin wasu mutane na cikin duniya dake zalinci da cin Amana basa tuna ranar da ALLAH zai kamasu ,yyi musu hukunci,wato a.....ke dallah rufemin baki!dak'kiya!uwar me kika sani,dazakice zakiyawa wani waazi....hmmm kiyi hakuri hjy Ni bance Miki inawa wani waazi ba... mittsss mom taja tsaki hade da cewa kikulamun da yaro na canxo kaya mutafi asibiti ta fad'a had'e da shafa kan Abdallah ta fice...

Abdallah kuwa duk abinda sukeyi yanajinsu da tambayar mom data Masa, sannan da amsar da riyan ta Bata yatsaya Masa arai yakuma yiwa amsar tata fassarori da yawa,saidai Kash bazai iya mgn ba ,balle ya tambayeta dalilin bawa mom wanna amsa...

Mom na fita"da hanxari riyan ta d'auki d'aya dg cikin wayoyin Abdallah dake kan bed side dirowa" talalubo number in Hafiz sbd tasanar Masa"aganinta Hafiz be kamata ace besan meke faruwa ba" tasaka Kira bugu2 yad'aga Yana cewa my man....bashi bane riyan ce...nan tashiga sanar dashi abinda yafaru...cikin tashin hankali Hafiz ke ta salati had'e da cewa dama Ina hanya bara na k'araso....ah ah yah Hafiz kabarshi,yyi saurin cewa meyasa?
Kallon Abdallah tayi haryanzun idonsa arufe...abinda Bata saniba! duk yanajin ta ,yaji dad'in sanarma da Hafiz datayi " cikin inda inda tace um muhade a hospital sbd can zamu!ok yace had'e da datse Kiran domin yagane cewa cikin2  dole guda ko mom ta hana asanar Masa ko Kuma tana Gurin ta nuna bataso yazo...
Riyan kuwa tak'i fad'a Masa mom ce taha na sbd ganin Abdallah k'ila yanaji tasan Kuma bazaiji dadiba....saurin aje wayar tayi sbd jin motsin za'a shigo.,,,,,,

    Mom ce da Abba,abayansu ya'u direba ne,cike da tausayawa suka Kama Abdallah suka fito da shi sbd asakashi mota,juyawa riyan tayi sbd taje ta sako hijab tabisu"mom ta dubeta had'e da cewa Ina zuwa?"

"Xanje nasaka hijab be"ta fad'a atakaice.

Baza kijeba , sbd zuwanki beda wani amfani agaresa ko agaremu,Bata jira amsarta ba ta fice dg d'akin"

Shiru riyan tayi had'e da Zama ,tana mamakin halin mom"kafin ta d'auki wayar Abdallah tasaka number in umma ta Kira.

 sallama umma tayi ,muryar riyan taji"murmushi tayi tace oh riyan kwana2 ya gdn?nan suka gaisa cike da alhini riyan ke sanar da umma lalurar datashafi Abdallah..

Cikin tausaya had'e da damuwa ,umma ta jajanta Mata had'e da cewa insha ALLAH acikin satin nan zatazo taga Abdallah d ajikin,nan suka Yi sallama umma nata kwantar Mata da hankali.

   ****  ****  ****
Hafiz byn sun gama waya da riyan,Kai tsaye asibitin da amminsa ke aiki ne yanufa sbd yasan da wuya Suki zuwa can sbd tafi kusa dasu Kuma asibiti ce maitsada da kula.

Office din ammin yanufa ,tana duba patient,amatsayinta na babbar likita k'wararra"da mamaki ta amsa sallamar sbd basudade da rabuwaba yazo gaisheta"saidai yanayin data gansa tasan tabbasa bbu lfy! agaggauce ta sallami patient d'in"kafin ta dubesa tace lfy dai ko Hafiz?"

Cikin damuwa had'e da tausaya wa ,yashiga yimata bayanin matsalar Abdallah.

Kafin tayi mgn anyi Knocking"

Yes "kawai tace,wata nurse ta shigo had'e da cewa Dr kije emergency da gaggawa anason ganinki sbd ankawo wani patient  Kuma doctor's da yawa akeson sutsaya akansa!

Ok kije ganinan zuwa"cewar ammin (Dr naja'at haruna)ta fad'a had'e da mik'e wa tsaye tasaka farar riga saman hijab nata ,kafin ta dubi Hafiz tace bara naje k'ila Abdallah ne.


Tashi yyi hade da cewa to mom muje nima na gansa"

Atare suka fito har zuwa kofar da zata sadaka da shiga emergency d'in... adedenan suka Sami Abba da mom had'e da ya'u direba, suna Kai komo" kallo d'aya zaka musu ka gano tsantsar tashin hankali acikin idanunsu....


     Gun Abba Hafiz ya nufa , yyinda ammi ta nufi ciki kawai,dukda ta lura da mom na Mata kallon sani ,Amma saita waske ta nunama batasanta,dukda cewar akwai abota mai k'arfi atsakanin yaronsu to Amma basu tab'a ganin junaba,dukda ita ammin tasan mom ce mahaifiyar Abdallah .

Rungume Abba Hafiz yyi Yana kuka tamkar karamin yaro"

Bubbuga bynsa Abba keyi cikeda da rarrahi yace kayi hakuri insha ALLAH abokinka zai Sami lfy "addua zami yimasa ba kukaba"cikin gamsuwa Hafiz ya d'aga Kai.

Gum mom ya isa ,ya gaida ita, had'e da Mata jaje"

Fuska bbu yabo bbu fallasa ta amsa,tana mamakin ya'akayi yasani?"kasna zuciyarta nace wa Anya waccen matar ba naja'at bace?

Da wannan tunanane tunanen takira hjy ikilima ta sanar da ita halin dasuke ciki"
Sannan suka zauna jiran fitowar doctors din dake kan Abdallah.

Hafiz kuwa office d'in ammi ya koma , yafito da wayarsa yakira layin Abdallah da riyan ta kirasa dashi yaji miyasa batazo asibitin ba.

Riyan dake zaune jugudum a parlou..taji wayar na ringing,dubawa tayi,ganin Hafiz ya sakata saurin d'agawa,bbu wani boye boye tasanar dashi mom ta hana, girgiza Kai yyi had'e da kashe wayar"

     #######

Kusan awa3 da wani Abu dashigar da Abdallah ,amma bbu wani Dr daya fito duk sub abba sunyi jigum jigum,tun safe ga shi har 1:saura.
Nan wasu doctors 2 suka fito suna sharce gumi"da hanxari Abba yanufeso har Yana tuntub'e"mom na Mara Masa baya
,Har suna had'a Baki Gurin cewa Yaya jikinsa?meke damun da?"

Girgiza Kai sukayi had'e da cewa ku kwantar da hankalinku,Dan ALLAH!yanxun zamuje muyi Sallah kafin mu ida bincikenmu "

Jiki asanyaye Abba yace to shikenan,kafin Yadubi mom cikin damuwa yace bara naje nayi Sallah,kiyi waya agd akawo wani abun bukata"

To "kawai tace,kafin ya fita"


Tana nan zaune Hafiz ya iso gurinta,Yana cewa mom Yaya dai jikin nasa?"

Cikin yatsina tace da sauk'i, had'e da cewa zaman me kake a hospital d'in nan?

Cike da mamaki azuciyarsa,yake sauraronta,Amma be nuna ba,sai yace na tsaya sbd naji yajikin Abdallah ne..Kuma nima ammina,wato mahaifiya ta anan take aiki..da sauri tace ko itace naja'at Musa ?"
Har zai ce eh ,sai kawai yatsintsi kansa da cewa ah ah itadai Dr naja'at haruna ta ke"

Ajiyar zuciya mom tayi ,wadda basan cewa hafis yajiba,tace ok inaga kamace.


Shikuwa Sarai Hafiz yasan ada da naja'at Musa take bearing ,byn abbansa yarasu ta maida da sunan mahaifinta ,wato naja'at haruna.
Sannan ya boyewa mom ne sbd besan miyasa take son sanin ammice koba amminceba gashi tasaki ajiyar zuciya to meke faruwa ne?Amma in hankali ya kwanta zai tambayi a mmi d'in.

Sallama yyimata akn xeje yyi Sallah.

Bayan awa3,hakan yyi Dede karfe 3:25pm, doctors d'in sufa fito sunata sharce gumi.

Da hanzari su Abba suka taresu,Dr naja'at ta cire eye glass d'in ta tace kusameni a office"Bata jira amsarsuba ta nufi hanyar office d'in ta da wani likita ,da alama ita dashi ne zasuyiwa su Abba bayanin ciwon dake damun Abdallah.

Babu Bata lokaci su Abba suka rufa masu baya zuwa office d'in.

Share 

BY
MMM FAREESA
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

  ๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written by mmn fareesa


Wannan shafin nakine halak malak Queen minart๐Ÿฅฐ๐Ÿ˜˜ kiyi yadda kikeso dashi...


Not edited

   P 25

""Bayan duk sun zauna koya ya nutsu"kafin Dr naja'at ta Fara mgn kamar haka...da farko dai Alh inaso kuyi hakuri ku maida lamarinku ga ALLAH ta hanyar karb'ar k'addararku daya k'addareku da ita! sannan kucigaba da Masa addua sbd shi ciwo lokaci guda yake shiga jikin mutum ,Amma sauk'i ahankali yake zuwa ind....ya isa haka pls kusanar damu Mike damun yaron mune?"cewar mom dake kallon Dr naja'at dake musu bayani"Dr naja'at Bata kalletaba da dubi Abba dake kallon ta tace maganar gsky Alh bazan boye maka ,munyi iya bakin kok'arin mu zurfafa bincike naganin munsan meye ke damun d'anka "Amma amsar guda ce"cikin k'osawa mom tace meye amsar?"
    Dr naja'at ta cigaba da cewa binkicenmu yanuna Mana cewa Yana cikin koshin lfy!abad'ini kenan"azahiri kuwa idanunsa kawai ke aiki ajikinsa, sannan abinda muka gane yanxun na damun shine jininsa Yana kok'arin yahau, Kuma zuciyarsa na bugawa.
Hakan Yana nuna alamar cewa yasaka damuwa aransa ne,Kuma munyi kok'arin shawo kan wannan matsalar...salati kawai Abba ke maimaita sbd tashin hankalinsa yakaru akan nada, yyinda mom keta kuka da surutai..
Dr kamar yadora da cewa duk asibitin da zaku kaisa indai tsakani da ALLAH zasu gaya muku to amsar d'aya ce da nan "sannan ayanzun abincinsa yakasance me ruwane sbd be iya motsa bakinsa balle har yatauna abinci"zamu rik'e sa sai zuwa gobe musallamesa"Amma dai yanada iyali ko?"eh yanada Mata ,cewar Abba kafin mom ta yi mgn yarugata.
  Dr Kamal yace ok to yakamata tazo kusa dashi sbd Yana bukatar kulawarta amatsayinta na iyalinsa,tunda yanxun komai sai anmasa.,,,,,

Insha ALLAH yanxun inmunyi la'asar zamuje adakkota tana gd"cewar Abba Yana duk'ar da Kai sbd  ganin yadda  mom ke jifansa da kallon tuhuma"


Gyaran murya Dr naja'at ta yi hade da cewa inada shawara Alh!

Abba yadubeta ya ce miye shawarar likita?

Gsky ciwon danku bana asibiti bane,ayadda na fahimta,ciwonsa na....ah ah dakata bamasan Jaye Jaye tunda kun kasa gane abinda ke damunsa inkun sallamesa zamu can za hospital ko mufitar dashi waje..cewar mom tana tashi tsaye.

Murmushi Dr naja'at ta yi domin yanxun ta lura mom ta daina Mata kallon sani,Kuma itama bazata nuna ta Santana,sai kawai tace to shikenan hjy ALLAH yasa adace" cikin Shan k'amshi mom ta ce Amin"sbd azatonta k'ila Dr naja'at ta ji shakkuntane...

Atare mom da Abba suka fice dg office d'in Dr naja'at.

Hafiz dke cikin toilet d'in office d'in yyi ajiyar zuciya sbd yaji komai ,ya fito zuciyar sa cike da tausayin abokin nasa.

Saurin dubarsa ammi tayi had'e da hararan sa tace har kabani tsoro,miye anfanin hakan kamana labe?

Murmushi Hafiz yyi had'e da cewa yi hkri ammi inason jin abinda ke damun AK ne"

Ok to kaje gd hakan nan tunda kaji,tun safe kake nan ,itama fiddausi yakama ta kaduba kaga halin datake ciki"

Zan tafi ammi Amma Dan ALLAH Zan tambayeki?"

Ina jinka "miye tsakanunku d hjy hafsat (mom) mahaifiyar Abdallah?"

Murmushi ammi tayi had'e da cewa meyasa kamun wannan tambayar?

Nan yashiga sanar Mata yadda mom ta tambayesa akan ta.....ajiyar zuciya ammi tayi had'e da cewa Zan sanar dakai wacece HASSU TSIYA TSABA! amma ba yanxunba ,abinda nikeso dakai kada ka nuna Mata cewa nice naja'at Musa,kanajiko?"eh ammi
   Ok zaka iya tafiya...

     *******

Abba d mom na fita takama balbalesa da masifa akan wane dalili zai ce Abdallah nada iyaline?"
Girgiza Kai yyi Kai tsaye yace basa abinci ,wanka , alwalla,kulada abinda yashafi tsiraicinsa ke Zaki kula Masa da sune?"
Tabe baki mom tayi had'e da cewa eh hakane muje to sai akawota nan d'in"ta fad'a. Cike da mamakin Wai yau Abba ke gaya Mata mgn a tsaye lallai da sake....
    Saida suka sake zuwa d'akin da akaje Abdallah ,suka samu Yana bacci ga drip an d'aura masa
Kafin su fice dg room d'in sukabar ya'u direba agunsa....
Byn Abba yyi Sallah suka nufi gd shida mom...

Byn mom tayi wanka tasaka zulfa ayi Mata Kiran riyan.
๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ

๐ŸŒบ AUREN WATA SHIDDA๐ŸŒบ

๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ๐Ÿพ


Story & written
by mmn fareesa


Not edited

p 26

Riyan na zaune kan abin Sallah yana azkar,byn ta idar da sallar la'asar wacce ta dad'e tanama Abdallah addua ,kafin ta soma azkar yyinda k'asan zuciyarta ke tunanin Yaya jikin Abdallah da sauk'i ko bbu?"
   Knocking d'in da taji ne yasaka cewa ashigo...byn zulfa ta shigo tasanar da ita Aiken mom kafin ta fice...
Tab'e baki Riyan tayi had'e da tashi ta ajiye cazbaza d'in,kafin ta fice ta nufi part d'in mom.",,,,,

   Fuska bbu yabo bbu fallasa tayi sallama had'e da Zama kan carpet tace ganiiii!
Cike da mamaki mom ke dubarta sbd ta lura dg yau da safe zuwa yanzun wani hayak'in rashin kunya ko me Riyan keji,Amma sai Bata nuna mamakin ta,tadaiyi kwafa azuciyarta sbd gab riyan din take da barin gdn...
Ayatsine tace abinda Zan gaya Miki shine kishirya yanzun ki dauki abinda zaku iya bukata keda my son" acikin driver's din my son wani zai kaiki hospital gurnsa ki kula dashi kafin muzo anjima nida abbansa!
     To insha ALLAH"riyan ta fad'a had'e da tashi ta fice"mom ta rakata da harara...
Bbu bata lokaci riyan ta shirya cikin doguwar riga ta amfa red tasaka hijab red,kafin ta fito taje bed room d'in Abdallah ta fito Masa da kayansa irinsu vest boxers jallabiya sbd tasan be wuce su mom take nufi ta fito Masa dashiba.... sannan ta Kira Hafiz tasanar Masa su had'u a asibiti "yace to...

     Basu iso abitinba sai kusan 5:12pm "har room d'in da Abdallah ya ke driver d'in yanunama riyan , sannan ya tafi"cikin faduwar gaba ta murd'a kofar tashiga,bakin ta d'auke da sallama.... Hafiz ya amsa Yana kallon ta "byn sun gaisa ta ce yamai jikin?Yadubi Abdallah dake jingine da pillow bisa gado yace da sauk'i...
   Matsowa tayi jikin gadon tana kallonsa tace yajikin?" ALLAH ya baka lfy" k'uri da ido yyi Mata Yana hongo tsantsar tausayinsa acikin k'wayar idonta,Wanda be tsammaci hakanba,azatonsa k'ila ma tace dole sai yasaketa Amma gashi ita rashin lafiyarsa tadameta....Yaya Hafiz ya ci abinci kuwa da wanka da Sallah???
Tambayar da riyan tayi ta sakashi dawowa tunaninsa,yanadaita aikin kallonsu..

"Ahankali Hafiz yace ah ah be jima da falkawaba ai"dama fresh milk ce da tea akace mu basa to komai dai akwai shi"to bara na had'a Masa tea din sai yyi Sallah da wanka.

Ok toshiken, Hafiz ya fad'a had'e da matsawa kusada Abdallah sbd byn farfadowarsa Yana Masa nasiha akan ya rungumi k'addararsa,dadai nasiha anan yafahimci yanajin mgn ,bede iyayinta"
Ahankali yace my man inason in sanar da Kai wata shawara Dan ALLAH inbacin nida riyan kada ka nunawa kowa kanajin mgn,inafatan kagane?"
Da ido Abdallah yace sbd me?
Hafiz yace Zan fad'a maka Amma da sauran lokaci... adedenan riyan ta iso da cup d'in tea mai kauri a hannunta ta dubi Hafiz tace gashito"
Gira ad'age yace nayime dashi?"
Kabashi yasha  Mana" 
Ke Kuma kiyi me Inna basa?"haba riyan! aike yakamata kibasa kinji"
Batace komaiba,taja kujerar roba Fara dake cikin d'akin ta matsa sosai kusada Abdallah dukda tanajin faduwar gaba ,haka ta daure, Hafiz ya d'ago kansa"had'e da bud'e Masa Baki har ya shanye duka Yana kallonsu da ido,kafin ta sake fito da fresh milk itama ta dura nasa , sannan ta basa ruwa yasha ...

Byn kamar minti12 , Hafiz ya fice dg room d'in"

Bbu jumawa yadawo shida wani doctor da keke me kujera suka Kama Abdallah suka aza akai"Hafiz ya shige dashi toilet sbd yyi arwala ya Rama sallolin dake akansa tunda Yana a haiyacinsa.

Bayan shigarsu riyan ta gyare gadon had'e da share room d'in sbd tasan Abdallah bayason k'azanta.


Bata jima da gamawaba suka fito, Hafiz ya saitashi ga alk'ibla yaga batarda Sallah dg zaune sbd lalurarsa...

Bayn ya idar ne Hafiz ya turasa acikin toilet , yafito Yadubi riyan yace kije kiyi Masa wanka"Amma kibi ahankali kada yashaki sabili inkin gama Masa ki fito ,sai nazo na fito da shi"
Zaro ido riyan tayi had'e da cewa wankafa?"girgiza Kai Hafiz yyi had'e da cewa eh riyan ai mijinkine ko?"Kuma akwai boxer ajikinsa....batasan sadda tasaki ajiyar zuciya ba.
Duk anacikin wani hali Saida hafis ya murmusa.


Kafin ta shige toilet d'in atsorace.

Zaune yake kan keken idonsa arufe,sbd jin k'arar bud'e kofar yasan itace saiyai maza ya rufe idonsa,dukda yasan akwai boxer ajikinsa sai yaji nauyin tagansa ahaka musammun sai yadda tayi dashi....wani imani yaji yasake shigarsa lallai rayuwa abun tsoroce "Wai ita wace irin mutumce yanxun duk rashin kwautatawar da yyimata ,bazaisa ta cusguna masaba  kota goranta Masa sbd yanzun Yana k'asa..
Wata zuciyar tace sbd ita daban take"Kuma zuciyarta tsarkakakkace tasan ko ita Bata wuce ALLAH ya jarabetaba.....tunaninsa ya tsaya cak sbd jin hannunta da soso ajinsa tana murzawa....


   Kofar toilet d'in aka Fara budewa ,kafin ta turosa akan keken,da Abba suka hade ido yyi tagumi cike da tausayi yake dubarsu...
Hafis ne yatashi yataimaka Mata suka saukeshi dg kan keken suka aza kan bed.

Kafin Abba yadubeta fuska asake yace sannu !kinji ALLAH yyimiki albarka yabaki ladar"
Fuska aduke tace Amin.

Abba ya matsa kusada da Abdallah ya rungumesa Yana Masa adduar samun lfy had'e da nasiha akan ya yadda da k'addara  "
Kallon sa Abdallah keyi yanason yace Masa Ina mom?"ai azatonsa bazata iya yin nesa dashi Kona na 1minit ba Yana cikin wannan halin"ALLAH sarki riyan ! yarinyar dayake wulakantawa gashi ita tafimasa mahaifiyarsa,sai yanzun ya tunada da nasihar Hafiz agaresa daya ke Masa fadan yadaina wulakanta riyan sbd D'an Adam darajace dashi bakasan Wanda zai maka Rana ba!gashi yagani ya wulakanta ita Kuma ta taimakaesa.... lallai bazai tab'a mantawa da Hafiz da riyan arayuwarsaba , wadanda yatabbatar bbu wad'anda mahaifiyar sa ta tsana sama dasu arayuwarta... wasu hawayene masu zafi na tausayin kansa suka Fara ziraromasa agefen ido....

Cikin dubara Hafiz ya goge Masa sbd kada Abba yagani.

Da taimakon Abba da Hafiz aka shirya Abdallah cikin t shirt da wanso 3 quarter...

Gab da magrib ,Abba da Hafiz suka fice zuwa masjid,sukabar Riyan agunsa ita kadai.

Itama alwarlal tayi bayn ta saita Abdallah dake kan keke a alk'ibla.

Bayan sun idar ,riyan na kan abin Sallah tana lazimi kafin lokacin isha'i yyi.

Afusace aka   banko kofar ,bbu ko sallama.

Da sauri riyan ta d'ago kanta Dan ganin su wayene.

Zeenat ce da hjy ikilima,suna jifar riyan da mugun kallo.

Wani faduwar gaba riyan ta ji Amma saita dake.

Abdallah na.....


Share

BY 
MMN FAREESA.

Comments

Popular posts from this blog

SIRRIN GANYAN ZOGALE (MORINGA)

CUTAR DA ISTIMNA'I YAKE YIWA ZAKARIN DA NAMI DA LALATA FARJIN MACE TARE DA MAGANIN SA